Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya. 03/10/2024

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Abdullahi Bello da Isiyaku Muhammed

  1. Wata wuta ta tashi a asibiti a Taiwan

    Wata wuta da ta tashi a asibitin kudancin Taiwan ta kashe mutum tara.

    Hukumomi sun ce wutar ta tashi ne bayan da gagarumar guguwa ta mamaye yankin, lamarin da ya kawo tangarɗa ga aikin ceto.

    Wakiliyar BBC ta ce har yanzu dai ba a iya gano dalilin da ya haifar da gobarar ba, sai dai rahotannin cikin gida na cewa wutar ta tashi ne sakamakon matsalar wutar lantarki.

    Guguwar ta kwashe kwana biyu tana shawagi a kudancin gabar tekun Taiwan, kafin daga bisani ta afkawa yankin. Break

  2. Biden na tattaunawa da Isra'ila kan barazanar kai wa Iran hari

    Biden

    Shugaba Biden na amurka ya ce yana tattaunawa da Isra'ila kan barazanar da ta ke na kai hari kan ɓangaren makamashin Iran a matsayin martanin hare-haren makamai masu linzami da Iran din ta kai wa Isra'ila.

    Ya ce ba umarni Amurka ke ba Isra'ila ba wajen kai hari, "illa kawai muna ba ta shawara ce, kuma yau babu abin da zai faru," in ji shi.

    Batun na Biden ya sa farashin ɗanyen mai ya tashi da kashi biyar cikin dari nan-take a kasuwar duniya.

    Tun bayan kai harin na ranar Talata an samu tashin farashin ɗanyen man da kashi 10 cikin ɗari.

    Ƙasar Iran ita ce ƙasa ta bakwai a duniya wajen samar da mai, inda take fitar da kusan rabin man da take samarwa, yawanci zuwa China

  3. Isra’ila ta faɗi ƙarin sojojinta da aka kashe a Lebanon

    Isra’ila ta sanar da kashe wani jami’in sojanta a kudancin Lebanon inda yanzu sojoji 9 ne adadin da ta ce an kashe a artabu da Hezbollah.

    Sai dai a sanarwar Isra’ila da ta fitar ba ta yi ƙarin bayani kan mutuwar sojan da ta ce kaftin ne.

    Amma a nata ɓangaren, Hezbollah ta Lebanon ta ce sojojin Isra’ila 17 ta kashe a artabun da suka yi a kudancin Lebanon a yau Alhamis.

    Wannan na zuwa bayan Isra’ila ta sha alwashin ci gaba da kai wa Hezbollah hare-hare ta kasa da sama.

    Isra'ila

    Asalin hoton, Reuters

  4. Abinci mai gina jiki ya ƙara tsada a Najeriya - NBS

    Hukumar ƙididdiga a Najeriya NBS ta ce an samu ƙaruwar hauhawar farashin abinci mai gina jiki a kasar.

    A rahoton da ta fitar ranar Alhamis, hukumar ta ce matsakaicin abinci mai lafiya da mutum ɗaya zai ci ya kai N1,255 a watan Agusta idan aka kwatanta da Yuli da ya kai N1,265.

    Hukumar ta ce alƙalumman sun shafi abubuwan da aka samar a gida da suka cika sharuɗɗan na abincin da ya dace a duniya.

    Hukumar ta kuma ce a kudu maso yammaci ne tsadar ta fi yawa inda abincin mutum guda a rana ya kai N1,554, sai kuma yankin kudu maso kudu inda abincin mutum ɗaya a rana ya kai N1,381.

    Rahoton ya ce yankin arewa maso yammaci ne lafiyayyen abincin da mutum zai ci a rana yake da sauki inda ya kai N1,014.

  5. An dakatar da wata jarida a Tanzania bisa zargin saɓa doka

    Tanzania

    Asalin hoton, AFP

    Tanzaniya ta dakatar da wata jaridar intenet ta The Citizen, bayan da ta zargi jaridar da wallafa abun da ya saɓa dokar ƙasar.

    Jaridar ta wallafa wani bidiyo a ranar Talata, mai ɗauke da ƙorafe-ƙorafe game da sace-sacen mutane da kashe-kashen da suka faru a baya-bayan nan.

    Hukumomi sun ce bidiyon ya ɓata wa ƙasar suna ya kuma karya doka. Jaridar dai ta goge bidiyon tun tuni tana mai cewa an yi wa bidiyon mummunar fahimta.

    Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan'adam sun soki lamarin da suka kira da take haƙƙin faɗin albarkacin baki.

  6. Kotu ta haramta wa VIO kamawa da cin tarar masu ababen hawa

    VIO

    Asalin hoton, @thecableng

    Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja babban birnin tarayyar Najeriya ta haramta wa hukumar bincike da kula da zirga-zirgar ababen hawa kwacewa ko kuma tarar masu ababen hawa.

    Alkaliyar kotun da ta zartar da hukuncin mai shari'a Nkeonye Maha ta ce babu wata doka da ta ba VIO damar tsayarwa ko kamawa da cin tarar ababen hawa.

    Wani lauya Abubakar Marshal ne mai rajin kare haƙƙin ɗan'adam ya shigar da ƙarar. Kuma kotun ta saurari kokensa inda hukuncin kotun ya ce "cin tarar ko wane irin abun hawa bai dace ba kuma ya saɓa doka.

    Kotun ta kuma yi umarnin hana duk wani mai aiki da yawun VIO ci gaba da keta haƙƙin ƴan Najeriya da ƴancinsu na walwala.

    "Kotu ce kawai ke da ƴancin saka tara kan abun hawa da aka kama da saɓa doka," a cewar alƙaliyar kotun.

    Sannan ta ƙara cewa hukumar da ke ƙarƙashin ikon ministan Abuja babu wata doka da ta ba su damar tsayarwa da kamawa ababen hawa tare da cin su tara.

  7. Rundunar sojin Lebanon ta tabbatar da kisan sojojinta biyu

    Rundunar sojin Labanon ta ce Isra'ila ta kashe sojojinta biyu a kudancin Lebanon.

    Rundunar ta ce an kashe soja guda a yayin gudanar da aikin ceto tare da ƙungiyar agaji ta Red Cross, inda gudan kuma ya rasu sakamakon harin da Isra'ila ta kai wa sansanin sojin ta sama.

    Sojojin sun ce sun mayar da martani nan take kan wadanda suka kai masu harin.

    Wakilin BBC ya ce sojojin Lebanon sun janye daga kan iyakar Lebanon da Isra'ilar a ƙoƙarinsu na kaucewa shiga yaƙin da Isra'ilar take da Hezbollah.

  8. Tsohuwar ma'aikaciyar BBC Hausa, Hajiya Fatima KIlishi ta rasu

    ..

    Asalin hoton, Yusuf Jamu

    Hajiya Fatima Kilishi Yari wadda a ake kira da Fatima Yusuf a lokacin da take aiki a BBC Hausa ta rasu a yau Alhamis bayan gajeriyar rashin lafiya.

    Marigayiyar ta fara aiki da sashen Hausa na BBC a birnin London a shekarar 1976 sannan kuma ta yi aiki da gidan rediyon Kano a shekarun 1980.

    Hajiya Fatima Kilishi ta rasu ta bar ƴaƴa da jikoki ciki har da mai taimaka wa gwamnan Kano kan hulɗa da jama'a, Hon Muhammad Jamu Yusuf.

  9. Iran ta zargi ƙasashen G7 da "rura wutar rikici" a Yammacin Asiya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan harkokin waje na ƙasar Iran, Esmail Baghaei ya zargin ƙungiyar ƙasashe bakwai masu ƙarfin tattalin arziƙi da "son zuciya da rashin dattako" dangane da sukar harin da ƙasarsa ta kai Isra'ila.

    Esmaeil Baghaei ya ce "ƙasashe bakwai masu ƙarfin tattalin arziƙi musamman Amurka na ƙara ta'azzara rashin tsaro da rashin zaman lafiya a yammacin Asia" saboda yadda suke bai wa Isra'ila makamai.

    A ranar Laraba ne dai ƙasashen bakwai masu ƙarfin tattalin arziƙi da suka haɗa da Canada da Faransa da Jamus da Iyaliya da Japan da Burtaniya da Amurka, a wata sanarwar haɗin gwiwa sun yi kakkausan suka dangane da harin da Iran ɗin ta kai wa Isra'ila.

    Ita ma ƙasar Iran ta kira jakadun Jamus da Austria da ke ƙasar a ranar Alhamis domin su bayar da bahasi kan sukar da ƙasashensu suka yi wa Iran ɗin.

  10. Burtaniya za ta miƙa ikon gudanar da tsibirin Chagos ga Mauritius

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Burtaniya ta amince ta miƙa ikon gudanawar tsibirin Chagos da ke tekun Indiya zuwa ƙasar Mauritius.

    An ƙulla yarjejeniyar mai cike da tarihi bayan shafe shekaru ana tattaunawa kan batun, inda a yau kuma firaiministan Birtaniya da Takwaransa na Mauritius suka fitar da sanarwar haɗin guiwa kan batun.

    A ƙarƙashin yarjejeniyar ƙasar Mauritius za ta bai wa Burtaniya aron tsibirin Diego Garcia na tsawon shekaru 99 domin ba da dama ga Amurka da Burtaniya su ci gaba da gudanar da sansaninsu na soji a tsibirin.

    Shugaba Biden ya yi maraba da yarjejeniyar inda ya ce hakan zai taimaka wajen tabbatar da tsaro a duniya.

    A bisa yarjejeniyar Mauritius za ta tsugunar da al'ummar Chagos ɗin waɗanda Burtaniya ta kora domin kafa sansanin soji.

    Jonathan Powell wanda jami'i ne a gwamnatin tsohon Firaiministan Buratniya Tony Blair, ya ce wannan matakin ya yi daidai.

    Ya ce abin da muka yi a shekarun da sittin 1960 ba daidai ba ne. Mun aikata abun kunya, shi ya sa gwamnatocin baya suka ba su takardar shedar zama ƴan Burtaniya.

  11. Hotunan rumfunan da wasu iyalai suka koma rayuwa a Beirut

    Beirut

    Asalin hoton, Abbas Salman/EPA-EFE/REX/Shutterstock

    Hare-haren Isra'ila sun tilasta wa mutane da dama barin muhallansu daga kudancin Lebanon.

    Hukumomi a Lebanon sun ce aƙalla mutum miliyan 1.2 ne suka bar muhallansu a sandiyar hare-haren.

    Birnin Beirut, inda mafi yawan waɗanda suke tsere daga muhallansu suka koma, ya cika, inda wasu yanzu suke samun mafaka a rumfuna da sauransu.

    Beirut

    Asalin hoton, Abbas Salman/EPA-EFE/REX/Shutterstock

  12. Jakar mataimakin shugaban kamfanin Thuraya ta ɓata a filin jirgin saman Abuja

    Rahotanni na cewa mataimakin shugaban kamfanin sadarwa na Thuraya Satellite Communication, Martin Kaufmann, bai ga jakar kayansa ba, bayan saukarsa a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Talata.

    Jaridar Punch, ce ta gano hakan a ranar Laraba inda ta ce an sanar da labarin sakamakon haɗin gwiwa da kamfanin na Thuraya da TSAT Communications Company.

    An dai gano Kaufman a wani taro ya sanya baƙar riga da wando mai launin ruwan toka.

    Da yake tabbatar da faruwar al'amrin, Kaufman ya kara da cewa hukumomin filin jirgin sun tabbatar masa cewa za a samu jakar tasa kuma za a kai masa ita.

  13. Matasa sun sake fita zanga-zanga domin neman a saki ƴan uwansu a ƙasar Ghana

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyoyin matasa a Ghana sun hau kan titunan biranen ƙasar domin yin zanga-zangar neman a saki masu zanga-zanga 50 da wata kotu ta bai wa ƴan sanda damar tsare su a makon da ya gabata.

    Wata zanga-zangar kwana uku ta nuna ƙin amince wa da haƙar ma'adanai a ƙasar ba bisa ka'ida ba ta janyo arangama tsakanin masu zanga-zangar da jami'an tsaro al'amarin da ya janyo aka kama masu zanga-zangar da dama bisa tuhumar haɗuwa ba bisa ƙa'ida ba.

    Da safiyar Alhamis ne kuma ɗaruruwan masu zanga-zangar suka yi dafifi inda suka hau titunan birnin Accra suna neman a saki mutum 50 ɗin da ake tsare da su.

    Mutanen ƙasar da dama dai sun alawadai da abin da ƴansandan da kotu suka yi na tsare matasan har tsawon makonni biyu.

    Ƙasar Ghana dai ita ce wadda ta fi kowacce ƙasa albarkatun gwal a nahiyar Afirka, to sai dai ƙasar tana fama da matsalar haƙar ma'adan ba bisa ƙa'ida ba wani al'amari da ya jawo gurɓatar muhalli ciki har da koguna.

  14. Shugaban Sudan ta Kudu ya kori shugaban hukumar leƙen asirin ƙasar

    Gen Akol Koor Kuc

    Asalin hoton, Eye Radio

    Shugaban Sudana ta Kudu, Salva Kiir ya kori shugaban hukumar leƙen asirin ƙasar, mai ƙarfin faɗa a ji, Janar Akol Koor Kuc.

    Ya zama shugaban hukumar - wadda ake matuƙar tsoro - tun bayan samun 'yancin kan ƙasar a 2011, inda ya ci gaba da jan ragamar hukumar a tsawon lokacin yaƙin basasar ƙasar da ya biyo baya.

    Sanarwar shugaban ƙasar ta cire shi daga muƙamin - da aka karanta a gidan talbijin na ƙasar - ba ta yi ƙarin haske kan dalilin cire shi daga muƙamin ba.

    To sai dai an naɗa shi gwamnan jihar Warrup - wadda mahaifar shugaban ƙasar ne - inda matsalar tsaro ke ƙara ta'azzara.

    Masu sharhi na cewa cire shi, wata alama ce ta yadda aka samu saɓani tsakanin manyan jagororin gwamnatin Kiir, inda wasu ke ganin Janar Kuc ka iya zama cikin waɗanda za su ƙwace mulki daga hannun shugaban mai shekara 73.

    Matakin na zuwa ne makonni bayan gwamnatin ƙasar ta sanar da ɗage zaɓen shugaban ƙasar - da aka tsara gudanarwa cikin watan Disamba - da shekara biyu.

  15. Isra'ila ta ce ta kashe manyan ƴan ƙungiyar Hamas uku a Gaza

    Rundunar sojin Isra'ila, IDF ta sanar da cewa ta kashe wasu manyan ƴan ƙungiyar Hamas guda uku watanni uku da suka gabata a Gaza.

    Daga cikinsu akwai Rawhi Mushtaha da IDF ɗin ta bayyana da shugaban gwamnatin Hamas da kuma Sameh al-Siraj da Sami Qudeh waɗanda ke da alhakin samar da tsaro ga Hamas.

    Rundunar ta IDF ta ce ta kashe su ne a wasu hare-haren sama da ta kai wurin da suke a ɓoye a ƙarƙashin ƙasa a arewacin Gaza.

    Isra'ila ta ce Hamas ba ta sanar da mutuwar mambobin nata ba "domin ka da ta karya wa mambobinta gwiwa".

  16. Lauyoyin Nnamdi Kanu sun buƙaci gwamnati ta janye masa zargin ta'addanci

    Kanu

    Asalin hoton, AFP

    Lauyoyin Nnamdi Kanu, jagoran ƴan awaren Biyafara, sun buƙaci gwamnatin Najeriya ta janye zargin ta'addanci da ake masa, ko kuma a bayar da shi beli domin ya samu isasshen lokacin shirya kare kansa.

    Lauyoyin sun bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, inda suka ƙara da cewa wanda suke karewa yana tsare ne a wajen hukumar DSS.

    Aloy Ejimakor, shi ne jagoran lauyoyin na Kanu, ya ce, "Inda ake cigaba da tsare shi a ofishin DSS ba shi da kyau sosai, kuma ba zai samu natsuwar shiryawa domin kare kansa a kotu ba a wajen."

    Lauyan ya ƙara cewa dalilin da ya sa Kanu ya buƙaci wancan mai shari'ar da ke sauraron shari'ar ta janye shi ne tunanin da yake cewa ana tauye masa haƙƙinsa na ɗan Adam, kuma ba a ba shi damar kare kansa.

    Shi ma barista Nnaemeka Ejiofor, ya ce abin da Kanu yake buƙata a yi masa ba raina kotu ba ne, illa kawai yana amfani da damar da kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada masa.

    Shi ma wani daga cikin lauyoyin nasa, Jude Uguwanyi ya alaƙanta cigaba da fama da matsalar tsaro da ake yi a kudu maso gabas da cigaba da tsare Kanu da gwamnati ke yi.

  17. An tura tsohon minista kurkuku a Singapore saboda karɓar kyaututtuka

    Singapore

    Asalin hoton, Getty Images

    Kotu a Singapore ta yanke hukuncin ɗaurin shekara ɗaya ga tsohon ministan sufurin ƙasar Subramanian Iswaran bisa samunsa da laifin rashawa da yi wa shari'a karan-tsaye - shi ne mutum na farko tsoho ko minista mai ci da aka ɗaure a ƙasar.

    Iswaran mai shekara 62 ya amsa tuhume-tuhume biyar da aka gabatar a kansa a makon da ya gabata, ciki har da batun karɓar kyaututuka da kuɗaɗensu ya haura dala dubu 300.

    Wakiliyar BBC ta ce bincike ya nuna cewa ya karɓi kyaututtuka daga manyan mutane da ƴan kasuwa da suka haɗa da tiketin zama kyauta a otel, tafiye-tafiye da wasu tarukan sharholiya.

    Masu gabatar da ƙara sun nemi a kulle shi na tsawon wata shida zuwa bakwai, amma masu kare shi sun nemi mako 8.

    Wannan shari'a ta Iswaran ta girgiza siyasar Singapore da ake mata kallon mai tsafta a idon duniya.

  18. Gwamnatin Najeriya ta cire harajin VAT a iskar gas da man dizil

    Tukunyar gas

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Najeriya ta sanar da cire harajin VAT a kan iskar gas da man dizil da sauran su.

    Ministan kuɗi, Wale Edun ne ya bayyana hakan a lokacin da yake bayyana wasu matakai da gwamnatinsu ta ɗauka domin rage wa ƴan Najeriya raɗaɗi.

    A wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama'a na ma'aikar kuɗi, Mohammed Manga ya fitar, wadda Daily Trust ta ruwaito, ya ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin na farfaɗo da ɓangaren iskar gas da man dizil da karya farashinsu.

    Sanarwar ta ce, "Gyara tsarin VAT na 2024 na nufin cire harajin VAT a kan wasu muhimman makamashi kamar iskar gas da man dizil da sauransu. Wannan matakin zai rage farashinsu, ya taimaka wajen samar da makamashi sannan ya sauƙaƙa wa ƴan Najeriya komawa amfani da su."

  19. Harin Isra'ila a wata makaranta a Gaza ya kashe mutum 22

    Gaza

    Gargaɗi: A wannan labarin akwai bayanai masu ɗaga hankali.

    Wani hari da Isra'ila ta kai a wata tsohuwar makaranta ya kashe ƙananan yara da dama, harin da aka ce ta kai ne domin wani mayaƙin Hamas, kamar yadda aka bayyana wa BBC.

    Rundunar Tsaron IDF ta ce wani kwamandan Hamas ne yake zama a cikin ginin.

    Harin ya yi ajalin mutum 22, ciki har da ƙananan yara 13 da mata shida, kamar yadda Ma'aikatar Lafiyar Hamas ta bayyana.

    An kulle makarantar ne domin zama sansanin gudun hijira ga waɗanda yaƙin ya raba da muhallansu.

    Wata ƙaramar yarinya mai suna Amal ta bayyana wa BBC cewa tana cikin makarantar lokacin da aka kawo musu harin.

    "Mu ƙananan yara laifin me muka yi? kullum muna cikin tashin hankali. Aƙalla ya kamata a ba makarantu kariya. Ba mu da gidaje, ba mu da makarantu, ina ake so mu je?"

    Wata majiya ta tabbatar wa BBC cewa an kashe wani ɗan Hamas a harin, wanda hakan ke nufin an kashe fararen hula da dama ne kawai saboda mutum ɗaya.

    Ita ma wata mata mai suna Huda Alhadada ta bayyana wa BBC cewa ta rasa yaranta guda biyu a harin.

  20. An kashe ƴan ci-rani shida a Mexico

    Mexico

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar tsaro a Mexico ta ce an kashe mutum shida da jikkata 10 lokacin da sojoji suka buɗe wuta a kan motar da ta ɗauko ƴan ci-rani.

    Ma'aikatar ta kuma ce motar ta yi ƙoƙarin kutsa kai shingen bincike na sojoji a jihar Chiapas da ke kudancin ƙasar.

    Ma'aikatar ta ce motar na ɗauke ne da baƙin-haure 33 daga ƙasashen Masar, Nepal, Cuba, Indiya da kuma Pakistan, "kuma ana ta rafka gudu da su, kamar an kwaso ɓarayi, sannan sai jami'an tsaro suka ji kamar ƙarar fashewar abu, wanda hakan ne ya sa suka buɗe wa motar wuta."

    Tuni aka ƙaddamar da bincike a kan lamarin, bayan an sanar da dakatar da sojojin da suka yi harbin.