Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 12/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 12/01/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Diginza, Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. Iran na neman tattaunawa da mu bayan barazanar kai mata hari - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce hukumomin Iran sun tuntubi Amurka domin neman tattaunawa, bayan barazanar da ya yi na ɗaukar matakin soji kan yadda ake kashe masu zanga-zanga a kasar.

    Trump ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da manema labarai, inda ya ce an riga an shirya wata ganawa tsakanin ɓangarorin biyu, amma kuma ƙila Amurka ta ɗauki wani mataki kafin a kai ga ganawar.

    A halin da ake ciki, wata kungiyar kare hakkin dan Adam a Iran ta ce ta tabbatar da mutuwar kusan mutum 500 tun bayan ɓarkewar zanga-zangar.

    Hakazalika, wasu faifan bidiyo da ke yawo sun nuna wani fili da ake ajiye gawawwaki a wajen Iran, inda jama’a ke zuwa domin neman gawarwakin ‘yan uwansu da suka ɓace.

  2. Hamas na shirin miƙa ikon Gaza ga kwamitin Falasɗinawa

    Hamas ta ce ta bayar da umarni ga dukkanin hukumominta na gwamnnati da cibiyoyi a Gaza, da su shirya mika iko ga wani kwamitin gudanarwa na Falasdinawa mai zaman kansa.

    Mai magana da yawun ƙungiyar, Hazem Qassem, ya ce hakan na daga tsarin da Shugaba Trump na kafa hukumar zaman lafiya da za ta tafiyar da mulkin Gaza,.

    Shirin na daga cikin kashi na biyu na yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta ta watan Oktoba da Isra'ila.

    A ƙarƙashin yarjejeniyar Hamas ta ce za ta janye daga mulkin yankin amma ta ƙi yarda da maganar zubar da makamanta.

  3. Jihohin Najeriya 5 da siyasarsu ke ɗaukar zafi gabanin zaɓen 2027

    Duk da cewa akwai sauran lokaci kafin zaɓen shekarar 2027, za a iya cewa harkokin siyasa sun fara zafi a Najeriya, musamman a wasu jihohin ƙasar da suka yi fice wajen siyasa mai zafi.

    A dokokin kundin hukumar zaɓen ƙasar ta INEC, har yanzu ba a fitar da jadawalin zaben 2027 ba, balle a san lokacin fara siyasa gadan-gadan.

    To amma tun daga shekarar da ta gabata ne siyasa ta ɗauki zafi a wasu jihohin Najeriya, inda ƴan siyasa suka riƙa sauya sheƙa, a wasu wuraren aka fuskanci hargitsi a wasu jihohi kuma ake ta musayar yawu.

    BBC ta yi nazari kan jihohin Najeriya da siyasarsu ke daukan hankali gabanin zaɓen na 2027.

  4. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Litinin da Hausawa ke yi wa kirari da Mande tushen aiki ko da nasara na tsaronki.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.