Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 23/01/25

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Isiyaku Muhammed, Rabiatu Kabir Runka

  1. Kamfanin Orano ya sake shigar da Nijar ƙara kan haƙar Uranium

    Kamfanin Orano na ƙasar Faransa ya sake shigar da sabuwar ƙara game da dambarwar da ke tsakaninsa na Jamhuriyar Nijar.

    Bayan buƙatar farko da aka ƙaddamar a watan da ya gabata bayan janye izinin aiki na ma'adinan Imouraren, Orano a wannan karon ya yi ƙarar ne yana neman a tabbatar da abin da ya kira haƙƙinsa.

    Kamfanin na Faransa wanda ya ƙwararre a fannin uranium, ya yi tir da yadda hukumomin mulkin sojan Nijar suka daƙile masa duk hanyoyin fitar da uranium daga wurin aikinsa na SOMAIR da ke ƙasar domin sayar da shi a kasuwanin duniya. Yanzu haka a wurin da ake ajiyar ma’adinan akwai sama da tan dubu ɗaya na ƙarfen uranium da darajar kuɗin shi ya haura Yuro miliyan 200.

  2. 'Trump na shirye-shiryen aika sojoji 10,000 zuwa iyakar Amurka da Mexico'

    Shugaban Amurka Donald Trump ya fara shirye-shiryen aika sojoji 10,000 zuwa iyakar ƙasar ta kudanci domin tabbatar da tsaron bakin iyakar ƙasar da Mexico.

    Tun da farko, an samu labarin cewa Amurka za ta aika sojoji 1,500 ne, amma ba za su shiga aikin "jami'an tsaron bakin iyaka ba", inda za su mayar da hankali ne wajen sanya shingayen kariya, wanda yana cikin shirin Trump na yaƙi da kwarorowar baƙi.

    A wata wasiƙar cikin gida ta hukumar kwastam da kare bakin iyaka, wanda ta fitar a ranar 21 ga Janairu - washegarin rantsar da Trump - ta nuna shirye-shiryen aika sojoji 10,000 domin taimakon hukumar wajen aikinta na kare bakin iyaka.

    Wasiƙar ta kuma ƙara da cewa akwai yiwuwar a yi amfani da sansanin sojin domin "tsare" baƙin haure da suka jiran a mayar da su ƙasashensu.

    Tun a ranar da aka rantsar da Trump ne ya sanar da dokar ta ɓaci kan bakin iyakar ƙasar da Mexico.

  3. ‘Damagum ba zai sauka daga shugabancin PDP ba sai a watan Disamba’

    Mataimaka shugabannin jam'iyya PDP na ƙasa sun ce shugabancin riƙon ƙwarya na Umar Damagun ba zai ƙare ba har sai zuwa watan Disamban bana.

    Mataimakin shugaban matasan jam'iyyar, Timothy Osadolor ne ya bayyana haka a madadin sauran mataimakan shugabannin jam'iyyar, inda ya ƙara da cewa dukkan masu adawa da shugaban su yi haƙuri har zuwa lokacin da wa'adinsa zai ƙare a watan Disamba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Sun ce suna kira ga waɗanda suke adawa da shugabancin Damagun su daina ɓata sunan jam'iyyar, su ba shi dama ya yi aikinsa.

    A game da muƙamin sakataren jam'iyyar, sun ce maganar na kotu, don haka suka ce Sanata Anyanwu ne suka ganin ya fi kamata ya riƙe muƙamin har zuwa lokacin da kotu za ta warware matsalar, sannan suka yi kira ga shugabannin jam'iyyar su haɗa hannu domin tabbatar da mulki ya dawo hannun PDP a zaɓen 2027.

  4. Likitocin Abuja sun buƙaci jami'an gwamnati su fara zuwa asibitocin gwamnati

    Likitocin Abuja waɗanda suke yajin aiki sun ƙalubalanci Ministan Abuja Nyesome Wike da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio su riƙa amfani da asibitocin gwamnati da ke babban birnin tarayya, Abuja domin sanin halin da marasa lafiya suke shiga.

    "Idan mun shirya gyara ɓangaren kiwon lafiya a ƙasar nan, ina tunanin ya kamata a tilasta wa jami'an gwamnati amfani da asibitocin gwamnati," kamar yadda shugaban ƙungiyar likitocin Abuja, George Ebong ya bayyana a tattaunawarsa da tashar Channels a ranar Laraba.

    "Zan so in fara ganin ministan yana zuwa asibitin Wuse, zan so ganin shugaban majalisar dattawa yana zuwa asibitin Maitama, sannan mu ga shugaban majalisar wakilai yana zuwa asibitin Nyanya. Idan aka fara haka ne za a iya gyara ɓangaren kiwon lafiya, amma matuƙar ba sa amfani da su, maganar gaskiya ba za a iya gyara su."

    Tun da farko, likitocin na Abuja sun faɗa yajin aiki ne a ranar Laraba saboda wasu haƙƙoƙinsu bayan wa'adin mako uku da suka bayar ya ƙare.

  5. Uba Sani ya mayar da sarkin da El-Rufai ya sauke

    Gwamnan Jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa Jonathan Paragua Zamuna rawaninsa na Sarkin Piriga.

    Gwamnan ya ce ya mayar wa sarkin rawaninsa ne bayan kotun ma'aikata ta jihar ta yanke hukuncin soke cire masa rawanin.

    A zamanin tsohon gwamnan jihar, Nasiru El-Rufai ne aka tuɓe rawanin sarkin, amma daga bisani sarkin ya kai ƙara kotu, inda a ranar 14 ga Yunin 2024, kotu ta soke cire sarkin, kamar yadda Channels ta ruwaito.

    Uba Sani ya taya sarkin murnar komawa kujerarsa, sannan ya yi kira a gare shi da ya yi adalci ga kowa ba tare da nuna bambancin addini da ƙabila.

    "Gwamnatinmu tana bin doka da oda. Wannan ne ya sa ba mu ɓata lokaci ba wajen ɗabbaƙa hukuncin kotun ma'aikata na mayar wa Sarkin Piriga rawaninsa," in ji shi.

    A nasa ɓangare, Sarkin Piriga, ya yi godiya ga gwamnan bisa mayar masa da rawani, inda ya ƙara da cewa akwai ƙabilu 12, kuma suna zama lafiya tare da juna.

  6. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sadarwa domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo da tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.