An kai wa ƴarmajalisar Amurka Ilhan Omar hari a Minneapolis
Wani mutum ya kai wa fitacciyar 'yar majalisar wakilan nan ta jam'iyyar Democrat a Amurka, Ilhan Omar, hari a lokacin da take gabatar da jawabi a wani taron wayar da kan jama'a a birnin Minneapolis.
'Yansanda sun ce mutumin ya yi amfani da sirinji ne wajen fesa mata wani ruwa da ba a san ko mene ne ba.
Ilhan wadda ta ci gaba da gudanar da jawabinta, ta ce ba za ta zuba ido tana kallon wadanda ta bayyana a matsayin karnukan farautar Trump su hana ta magana ba.
Wakiliyar BBC Ana Faguy, na cikin dakin taron lokacin da abun ya faru. Ta ce ''na ji shi mutumin na ta cewa tana so ne ta hada mu fada da juna, yayin da ake kokarin fitar da shi daga dakin taron.''
Wurin ya dan yi shiru, kafin daga bisani aka ci gaba da gudanar da taron.