Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/053/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku bayanai kan yaƙin Iran da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 25 ga watan Mayun 2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Ba a kammala cimma yarjejeniya da Amurka ba - Iran

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Iran, Esmail Baghaei, ya ce an samu ci gaba a tattaunawar da ake yi kan wasu batutuwa, amma har yanzu ba za a iya cewa an kammala cimma cikakkiyar yarjejeniya ba.

    Baqaei ya yi wannan bayani ne a martani ga maganganun jami’an ƙasar Amurka da ke cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar.

    Ya ce ɓangarorin biyu sun cimma matsaya kan wasu muhimman batutuwa, amma har yanzu akwai sauran abubuwa da ba a kammala ba.

    Ya kuma danganta rashin tabbas ɗin da ake ciki da saɓanin matsayi daga Washington da kuma tarihin rikice-rikice da ke faruwa a lokacin tattaunawa.

    Wannan na zuwa ne yayin da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce tattaunawar tana ci gaba kuma ba ta tsaya ba.

    Shi ma shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce an kusan cimma yarjejeniya,

  2. Ana fargabar farashin gas na girki zai ci gaba da tashi a Najeriya

    Ana fargabar farashin gas na girki zai ci gaba da tashi a Najeriya, yayin da ’yan kasuwa da masu amfani da shi ke fuskantar matsin lamba daga ƙarin tsadar kaya a sassan ƙasar.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Ƙungiyar ’yan kasuwar iskar gas ta Najeriya (NALPGAM) ta bayyana damuwa kan ƙarancin gas na girki da kuma tashin farashinta a faɗin ƙasar, inda ya kai har naira 1,500 kan kilo guda daga naira 1,300 a wasu yankuna.

    Ƙungiyar ta ce matsalar ta samo asali ne daga ƙarancin wadata da tsadar farashin iskar gas ɗin a tashoshi da matsalolin sufuri, da kuma ƙarin kuɗaɗen gudanar da kasuwanci da ke ƙara tsananta yanayin.

    A cikin sanarwar da ta fitar, ƙungiyar ta ce ’yan kasuwa suna sayen tan 20 na gas kan sama da naira miliyan 25 zuwa miliyan 26, lamarin da ke haifar da hauhawar farashi ga masu saye a kasuwa.

    Ta kuma yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba, matsalar za ta iya ƙara jefa gidaje da ƙananan kasuwanci cikin wahala, tare da haifar da hauhawar farashin abinci da koma-baya ga manufofin makamashi a Najeriya.

  3. Yau ake fara aikin Hajjin shekarar 2026

    A yau ne aka fara aikin Hajjin shekarar 2026 a ƙasar Saudiyya a daidai lokacin da yankin ke fama da tashin hankali sakamakon yaƙin Iran.

    Hukumomin Saudiyya sun ce sama da mahajjata miliyan ɗaya da rabi daga ƙasashen waje ne suka isa ƙasar domin gudanar da ibadar bana, adadin da ya zarce na shekarar da ta gabata duk da rikice-rikicen a ke ci gaba a yankin.

    Rahotanni sun kuma nuna cewa Saudiyya ta fuskanci wasu hare-hare tun bayan fara yaƙi tsakanin Iran da Amurka da kuma Isra'ila, abin da ya ƙara dagula yanayin tsaro a yankin.

    Domin kwantar da hankulan mahajjata, ma’aikatar tsaron Saudiyya ta fitar da bidiyo da ke nuna na’urorin kariya na sararin samaniya da aka girke a kewayen birnin Makka.

  4. An kashe sojan Isra'ila a Kudancin Lebanon

    Sojojin Isra’ila sun ce an kashe wani sojansu yayin fafatawa a kudancin Lebanon.

    Isra’ilar ta kuma sanar da cewa wasu sojojin sun samu munanan raunuka inda aka kai su asibiti domin samun kulawar likita.

    Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan yadda aka kashe sojan ko kuma inda arangamar ta faru ba.

  5. Farashin mai ya faɗi saboda fatan cimma yarjejeniya tsakanin Iran da Amurka

    Farashin ɗanyen mai ya faɗi sosai yayin da kasuwannin hannayen jari na Asiya suka samu ƙaruwa, sakamakon fatan cimma yarjejeniyar da za ta kawo ƙarshen yaƙin Iran.

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce a ranar Asabar ana ci gaba da tattaunawa sosai kan yarjejeniya da Tehran, yana mai cewa za a bayyana cikakkun bayanai nan ba da jimawa ba.

    Sai dai washegari ya gargaɗi tawagar masu tattaunawarsa da kada su yi gaggawar cimma yarjejeniya.

    A safiyar Litinin a kasuwannin Asiya, farashin ɗanyen man Brent ya sauka da kashi biyar cikin ɗari zuwa dala 98.36 kan ganga guda, yayin da ɗanyen man Amurka ya ragu da kashi 3.5 cikin ɗari zuwa dala 91.50 kan ganga.

    Trump ya taɓa cewa yarjejeniyar za ta haɗa da sake buɗe mashigar Hormuz, amma bai bayyana ƙarin bayani ba.

    Mashigin ruwan, wanda ake bi wajen jigilar kusan kashi ɗaya cikin biyar na man duniya da iskar gas ya kusa daina aiki tun bayan fara faɗan a ranar 28 ga Fabrairu.

  6. Majalisar Iran ta fara zamanta na farko tun bayan fara yaƙi

    Majalisar dokokin Iran ta fara zamanta tun bayan fara yaƙi, inda ’yan majalisar suka halarci zaman a zauren majalisa karo na farko cikin fiye da kwanaki 80.

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an gudanar da zaɓen shugabancin majalisar ne a yayin zaman.

    Tun bayan fara yaƙin Isra’ila da Amurka da Iran ne aka dakatar da zaman majalisar, inda aka gudanar da zama guda ɗaya kacal ta hanyar intanet

  7. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.