Ba a kammala cimma yarjejeniya da Amurka ba - Iran
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Iran, Esmail Baghaei, ya ce an samu ci gaba a tattaunawar da ake yi kan wasu batutuwa, amma har yanzu ba za a iya cewa an kammala cimma cikakkiyar yarjejeniya ba.
Baqaei ya yi wannan bayani ne a martani ga maganganun jami’an ƙasar Amurka da ke cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar.
Ya ce ɓangarorin biyu sun cimma matsaya kan wasu muhimman batutuwa, amma har yanzu akwai sauran abubuwa da ba a kammala ba.
Ya kuma danganta rashin tabbas ɗin da ake ciki da saɓanin matsayi daga Washington da kuma tarihin rikice-rikice da ke faruwa a lokacin tattaunawa.
Wannan na zuwa ne yayin da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce tattaunawar tana ci gaba kuma ba ta tsaya ba.
Shi ma shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce an kusan cimma yarjejeniya,