Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 17/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 17/01/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Ɗan Bobi Wine ya ce jami'an tsaro sun 'ɗauke' iyayensa

    Ɗangidan jagoran adawar Uganda ya ce sojoji da wasu jami'an tsaro na musamman sun sace iyayensa daga gidansu da ke Kampala.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na X, Solomon Kampala ya ce an ''ɗauke Bobi Wine da Barbara Kyagulanyi tare da kai su wani ɓoyayyen wuri.

    Wani makusancin Wine ya shaida wa BBC cewa jami'an tsaron sun shiga gidansa da ƙarfin tsiya sannan suka ɗauke a wani jirgi mai saukar ungulu.

    Tun farko Bobi Wine ya soki ingancin sakamkon farko na zaɓen shugaban ƙasar da ya gudana ranar Alhamis, wanda ya nuna Shugaba Yoweri Museveni ne ke kan gaba da gagarumar tazara, yayin da aka kusan kammala ƙirga ƙuri'u.

    Sai dai rundunar ƴansandan ƙasar ta musanta iƙirarin sace Wine.

    A yau Alhamis ne ake sa ran bayyana sakamkon zaɓen, wanda tuni ake hasashen Museveni ne zai lashe.

  2. Trump na naɗa kwamitin zaman lafiya da zai jagoranci Gaza

    Shugaban Amurka, Donbald Trump ya bayyana sunayen mambobin kwamitin da zai jagoranta, wanda zai tafiyar da zaman lafiyar Gaza.

    Daga cikin mambobin kwamitin har da sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio da tsohon firaministan Birtaniya Tony Blair.

    Sauran sun haɗa da surukinsa, Jared Kushner da kuma wakilin Trump na musamman a Gabas ta Tsakiya, Steve Witkoff da shugaban Bankin Duniya, Ajay Banga.

    Fadar gwamnatin Amurka ta ce akwai aikin musamman da kowane ɗaya daga cikin mambobin kwamitin zai yi, don taimaka wa zaman lafiyar Gaza.

    Shugaba Trump ne zai jagoranci kwamitin, yayin da wasu ƙwararrun ƴan Boko za su kula da kwamitin farar hula a Gaza.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo a shafukanmu na sada zumunta, domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.