Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da yake kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Ahmad Bawage, Nabeela Mukhtar, Abdullahi Bello Diginza da Isiyaku Mohammed

  1. Mutum shida sun mutu, 43 sun jikkata a harin Isra'ila a birnin Nabatieh

    Ma'aikatar lafiya a Lebanon ta tabbatar da mutuwar mutum shida a wani hari da Isra'ila ta kai birnin Nabatieh a safiyar yau Laraba.

    Ta ƙara da cewa mutum 43 ne kuma suka jikkata.

    Kamar yadda muka ruwaito da farko, ɗaya daga cikin mutanen da suka mutu sun haɗa da wani magajin gari wanda ke halartar wani taro a birnin.

  2. Harin Isra'ila ya kashe magajin gari a Lebanon

    Wani magajin gari na cikin mutane biyar da aka kashe a harin da Isra'ila ta kai a birnin Nabatieh na kudancin Lebanon a yau Laraba, kamar yadda wata majiya ta shaida wa BBC.

    Wani shaidan gani da ido ya bayyana lamarin a matsayin "ta'addanci", yana mai cewa aƙalla an kai hare-hare ta sama munana guda tara a birnin cikin mintuna 30.

    Ya ce hare-haren sun afka wa ginin karamar hukumar Nabatieh, inda magajin garin ke halartar wani taro domin shawo kan matsalar jin-kai a birnin.

    Shaidan ya kuma ce ya ga motocin ɗaukar marasa lafiya na kai kawo wajen da lamarin ya faru domin su taimaka da aikin ceto.

    Ma’aikatar lafiya ta ƙasar ta tabbatar da kai harin, inda ta ce adadin waɗanda suka mutu sun kai mutum biyar.

  3. Labarai da dumi-dumi, Mutanen da suka mutu a fashewar tankar mai a Jigawa sun ƙaru zuwa 104

    Mutanen da suka mutu sakamakon fashewar tankar mai a jihar Jigawa sun ƙaru zuwa 104.

    Shugabar hukumar kiyaye afkuwar haɗura ta jihar Jigawa, Aishatu Sa'adu ce ta tabbatar wa da BBC hakan.

    Ta ce kawo yanzu fiye da 100 kuma suna asibiti saboda raunuka da suka samu, inda suke ci gaba da samun kulawa.

  4. Hotuna: Isra'ila na ci gaba da ruwan wuta a Gaza

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi Alla-wadai da yawan fararen hula da aka kashe da kuma jikkata a Gaza a cikin kwanakin nan.

    Isra'ila ta ce tana ci gaba da kai hare-hare ne domin lalata wuraren Hamas.

    Waɗannan hotuna sun nuna yadda al'amura suke bayan hare-haren Isra'ilar.

  5. Labarai da dumi-dumi, An naɗa Tuchel a matsayin sabon kocin Ingila

    An naɗa Thomas Tuchel a matsayin sabon kocin Ingila. Kwantiragin zai fara ne daga 1 ga watan Janairun 2025.

    Ɗan ƙasar Jamus mai shekara 51, ya zama mutum na uku da zai jagoranci Ingila wanda ba ɗan ƙasar ba, bayan Sven-Goran Eriksson da Fabio Capello.

    Gareth Southgate ya yi murabus a watan Yuli bayan shan kashi da Ingila ta yi a hannun Sifaniya a wasan karshe na Gasar Euro 2024.

    Lee Carsley, wanda aka naɗa a matsayin kocin riƙon kwarya a watan Agusta, zai ci gaba da riko a wasannin Gasar Nations League da Ingila za ta yi da ƙasashen Greece da kuma Jamhuriyar Ireland a wata mai zuwa.

    Tuchel, wanda ya bar Bayern Munich a karshen kakar wasanni da ta gabata, ya ce: "Ina alfahari da wannan dama da aka ba ni na jagorantar tawagra Ingila.

    "Na daɗe da son irin salon wasa da ake yi a ƙasar nan, kuma tuni na fara jin daɗin matsayi da na samu," in ji Tuchel.

  6. An ceto wani mutum bayan shafe kusan wata biyu a cikin ruwa

    An ceto wani ɗan Rasha bayan kwashe sama da watanni biyu a cikin ruwa a wani karamin kwale-kwale a tekun Okhotsk da ke gabashin ƙasar.

    Jami’ai sun ce wani ma’aikacin jirgin ruwa ne ya gano mutumin mai suna Mikhail Pichugin mai shekaru 46 a duniya, kusan nisan kilomita 1,000 daga inda ya taso a farkon watan Agusta.

    Rahotanni sun ce an gano gawar ɗan uwansa da kaninsa mai shekaru 15 a cikin jirgin.

    Matar Mista Pichugin ta ce mutanen uku sun je teku ne don kallon yadda kifaye ke rayuwa kuma sun tafi da kayan abinci na tsawon makonni biyu.

    Ta shaida wa kamfanin dillancin labaran ƙasar Rasha Ria Novosti cewa nauyinsa na iya zama sanadiyyar ceto - yana da nauyin kilogiram 100 lokacin da suka yi tafiyar.

    "Ba mu san komai ba zuwa yanzu. Mun dai san yana da rai... Wani irin abin al'ajabi ne!" kamar yadda matar mutumin ta bayyana.

    Ta kuma ce dama ’yarsu ya kamata ta tafi da su a balaguron, amma ta yanke shawarar komawa gida.

    Wani jirgin sama mai saukar ungulu ya gano babu wata alama ta mutanen uku bayan da aka bayar da rahoton ɓacewarsu, a cewar Ria.

    An gano jirgin ne ranar Litinin yayin da ya ke zagayawa a gaban wani jirgin kamun kifi a gaɓar tekun Kamchatka da ke gabashin Rasha.

  7. Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

    Wasu da ake zargin ƴan bimdiga sun kashe mutum biyar a wani sabon hari da suka kai karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

    Shugaban ƙungiyar ci gaban al'ummar Bokkos, Farmasum Fuddang shi ya tabbaatr da faruwar hakan a jiya Talata.

    Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa irin harin ya janyo mutuwar mutane biyar bayan kwantan-ɓauna da ƴan bindigar suka yi musu.

    "Harin ya yi sanadiyyar rayukan matasa huɗu waɗanda suka fito domin tsare gidajensu. Bayan nan maharan sun kuma kashe wani tsoho bayan yin dirar miƙiya zuwa cikin gidansa," in ji Fuddang.

    Harin dai na zuwa ne ƙasa da mako ɗaya da kai wasu hare-hare, inda aka kashe wasu mutane goma a karamar hukumar ta hanyar yi musu kisan gilla.

    Al'ummar yankin sun yaba wa jami'an tsaro bisa ƙoƙarinsu na fatattakar ƴan bindigar, inda suka yi kira na a ƙara kaimi tare da haɗin gwiwa wajen daƙile irin waɗannan hare-hare a yankin.

  8. Labarai da dumi-dumi, Fashewar tankar mai ta kashe kusan mutum 100 a Jigawa

    Wata tanka ɗauke da man fetur ta yi sanadiyyar kashe kusan mutum 100 a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya bayan ta fashe tare da kamawa da wuta.

    Kakakin rundunar ƴansandan jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da mutuwar mutum 94 zuwa yanzu.

    Ya ƙara da cewa hatsarin da ya faru ranar Talata da tsakar dare ya raunata wasu mutanen kusan 50.

    Babbar jami'ar hukumar kiyaye haɗurra a Jigawa, Aishatu Sa'adu, ta shaida wa BBC cewa Ibtila'in ya faru ne a garin Majia da ke ƙaramar hukumar Taura bayan da direban tankar ya kauce wa wata babbar mota ɗauke da tumatur.

  9. Hezbollah ta harba gwamman makaman roka zuwa cikin Isra'ila

    Ƙungiyar Hezbollah ta ce ta harba gwamman makaman roka zuwa garin Safed da ke arewacin Isra'ila.

    Sojojin ƙasar sun ce sun gano wasu rokoki kusan 50, waɗanda aka kakkaɓo wasu daga cikinsu.

    Kawo yanzu dai babu rahoton asarar rayuka.

    Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Isra'ilar ta kai wani hari kudancin birnin Beirut da sanyin safiyar yau Laraba.

    Dama sojojin Isra'ilar sun ba da umarnin kwashe mazauna yankin nan take.

  10. Isra'ila ta kai hari birnin Beirut karon farko cikin kwanaki biyar

    Isra'ila ta kai hare-hare ta sama cikin dare zuwa Beirut, babban birnin Lebanon.

    Wannan shi ne karon farko da take kai harin cikin kwanaki biyar.

    Isra'ilar ta ce ta far wa wani gidan ajiya wanda Hezbollah ke amfani da shi wajen adana maƙamai.

    Harin na birnin Beirut na zuwa ne bayan da hukumomin Lebanon suka ruwaito cewa hare-haren Isra'ila sun kashe mutane a faɗin gabashi da kuma kudancin ƙasar.

  11. Buɗewa

    Ma'abota BBC Hausa barkan mu da hantsin Laraba - ta bawa ranar samu.

    Ku kasance da mu a wannan shafi domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da kuma sauran sassan duniya.