Mun samu barazanar kai wa majalisar dokokin Najeriya hari - Ɗanmajalisa
Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilan Najeriya, kan tsaron cikin gida, Garba Muhammad ya bayyana cewa ƴanbindiga sun yi barazar kai wa ginin Majalisar Dokokin ƙasar harin bam.
Yayin da yake jawabi a wani zaman sauraron ra'ayoyin jama'a kan ƙudurin dokar kafa hukumar tsaron majalisar dokokin ƙasar, ɗanmajalisar ya jaddada buƙatar gaggauta ƙarfafa tsaro a majalisar da ke zama cibiyar dimokuraɗiyyar ƙasar.
Hon. Garba Muhammad ya ce idan aka kafa hukumar za ta ƙula da tsare-tsaren tsaro da kare sanatoci da ‘yan majalisa da ma’aikata da baƙi.
Ya ƙara da cewa majalisar na fuskantar ƙalubalen tsaro masu yawa, ciki har da satar motoci da babura da lalata kayayyaki da amfani da katin shaida na ƙarya da kuma shiga harabar majalisar ba tare da izini ba.
“Mun samu barazanar ƴanbindiga da ke shirin kai harin bam a majalisar dokokin ƙasar, da kuma barazanar wasu masu zanga-zanga da ke son ƙulle majalisar." in ji shi.
“’Yan majalisa na fuskantar barazana daga wasu al’ummarsu da kuma wasu mutane da ke samun damar shiga ofisoshinsu ba tare da wani tsarin ganawa na hukuma ba.”
Ya yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakan gaggawa don magance irin waɗannan barazanar tsaro ba, hakan na iya haifar da cikas ga ayyukan majalisa, wanda zai iya yin illa ga tafiyar da mulki da kuma tsarin dimokuraɗiyya.