An bai wa Trump shawara kan matakan da zai iya ɗauka kan Iran, ciki har da na soji
An bai wa Shugaban Amurka Donald Trump shawarwari kan matakai daban-daban da zai iya ɗauka kan Iran, ciki har da na soji da kuma waɗanda zai iya ɗauka ta ƙarƙashin ƙasa, kamar yadda wasu jami’an ma’aikatar tsaron Amurka biyu suka shaida wa kafar yaɗa labarai ta CBS, abokiyar hulɗar BBC a Amurka.
Jami’an Pentagon sun ce har yanzu ana la’akari da yiwuwar kai hare-haren makamai masu linzami daga nesa idan Amurka za ta tsoma baki, amma an kuma gabatar wa Trump wasu matakan na daban da suka haɗa da kutse ta shafukan intanet da kuma dabarun sauya tunanin ƴan ƙasar ta Iran.
A ranar Litinin Trump ya sanar da sanya harajin kashi 25 cikin 100 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama ke cewa fiye da masu zanga-zanga 600 ne aka kashe cikin makonni uku na zanga-zangar adawa da gwamnati a Iran.
Ministan harkokin wajen Iran ya ce Tehran a shirye take domin tattaunawa da Amurka, amma ya jaddada cewa ƙasar “a shirye take da yaƙi” idan aka tilasta mata.
Ana sa ran ƙungiyar tsaron ƙasa ta Trump za ta gudanar da taro a Fadar White House a yau Talata domin tattauna matakan da za a iya ɗauka waɗanda suka shafi Iran, sai dai har yanzu ba a tabbatar ko shugaban ƙasar da kansa zai halarci taron ba.
A baya Trump ya ce sojojin Amurka na duba “matakai masu tsauri ƙwarai” na tsoma baki idan aka ci gaba da kashe masu zanga-zanga a Iran.