Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 08/07/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Talata 08/07/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Abdullahi Bello Diginza

  1. APC ta fara sayar da fom na zaɓukan cike giɓin ƴan majalisu

    Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta fara sayar da fom na takarar zaɓukan cike gibi na ƴan majalisu dokokin ƙasar.

    A makon da ya gabata ne hukumar zaɓen ƙasar INEC ta saka ranar 16 ga watan Agusta mai zuwa domin gudanar da zaɓukan cike giɓin ƴan majalisun dokokin ƙasar.

    Ana gudanar da irin wadannan zaɓuka domi cike guraben ƴan majalisun da suka mutu ko suka sauka daga kujerun saboda wani dalili.

    Hukumar zaɓen ta ce za a gudanar da zaɓukan ne a jihohin ƙasar 12.

    Tuni dai ƴan jam'iyyar ta APC suka fara zuwa sakatariyar jam'iyyar domin sayen fom na takarar.

    Jam'iyyar ta APC ta saka ranar 16 ga watan Yulin da muke ciki a matsayin ranar gudanar da zabukan fitar da gwani na waɗannan kujeru.

  2. Ana fargabar kashe ƴan banga 70 a harin kwanton ɓauna a Filato

    Rahotonni daga jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya na cewa ƴanbindiga sun kai harin kwanto ɓauna kan wasu ƴan banga tare da kashe aƙalla 70 a wasu ƙauyukan jihar biyu.

    Wani mazaunin yankin ya shaida wa BBC cewa sun gano gawarwaki 56 bayan harin.

    Sai dai bayanai na cewa akwai wasu ƴan bangar da damar da yanzu ba a gani ba, waɗanda ke fargabar sun mutu.

    Can ma a ƙauyen Banyun na na jihar wani mazaunin yankin ya tabbatar da kashe ƴan banga 10.

    Ya ƙara da cewa maharan sun kuma ƙona gidaje da dama da dukiyoyi.

    Bayanai na cewa tun bayan da hare-hare suka yawaita a wasu yankunan Wase, aka riƙa gayyato ƴan banga daga wasu yankunan jihar da ma jihar Taraba domin taimaka wa tsaron wasu ƙauyukan yankin.

  3. Babu wata cikas a tattaunawar tsagaita wutar yaƙin Gaza - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya dage cewa babu wani cikas da ake fuskanta a tattaunawar da ake yi na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, bayan da aka kammala zagayen karshe na tattaunawa tsakanin Isra'ila da Hamas ba tare da cimma wata matsaya ba.

    Shugaban na Amurka yana magana ne a lokacin da ya ke karbar baƙuncin Firaministan Isra'ila a wata liyafar cin abinci a birnin Washington.

    Fadar White House na ƙoƙarin sirrinta bayanan wannan ganawar ta Mr Trump da shugaban Isra'ila, saɓanin yadda ake yi da sauran shugabannin ƙasashen duniya.

    A nasa ɓangaren, Benjamin Netanyahu ya yi watsi da yiwuwar samun cikakken yancin Falasɗinawa, yana mai cewa dole ne "Isra'ila" ta ci gaba da kula da harkokin tsaro a Gaza.

  4. Adadin waɗanda suka mutu a ambaliyar Texas ya haura 100

    Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana cewa adadin waɗanda suka mutu sakamakon ambaliyar jihar sun zarta 100.

    Masu aikin ceto na ci gaba da lalubo gawarwaki, yayin da da kawo yanzu ba a iya tantance adadin waɗanda suka ɓace ba.

    A ranar Juma'ar da ta gabata ne wata mummunar ambaliya ta auka wa jihar sakamakon mamakon ruwan sama mai ƙarfin gaske haɗe tsawa.

    Masu gudanar da wani wurin shaƙatawa - da ambaliyar ta rasa - sun tabbatar da mutuwar ƴan mata 27 da ke wurin a lokacin da ambaliyar ta ratsa yankin.

    Wasu na ganin rashin ware isassun kuɗi wa ɓangaren kula da yanayi a kasafin kudin ƙasar ne ya haifar da matsalar, zargin da gwamnatin Amurka ta musanta.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiya.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a fain duniya.

    Kuna iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.