KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 30 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Ba za mu mutu ba idan ba mu ci gaba da sarrafa uranium ba - Iran

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Yousef Pezeshkian, ɗan shugaban ƙasar Iran Masoud Pezeshkian, ya ce rayuwar mutanen Iran ba ta dogara ne kan aikin sarrafa da inganta sinadarin uranium ba, yana mai cewa "idan ba mu yi hakan ba, ba za mu mutu ba."

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram, Yousef ya bayyana cewa ba ya adawa da sarrafa uranium, kuma yana biyayya ga duk wata shawara da Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran da kuma jagorancin ƙasar suka yanke.

    Sai dai ya ce ya kamata a fahimci dukkan fa'ida da illa kafin ɗaukar kowace irin shawara.

    Ya ƙara da cewa makamashin nukiliyar Iran ba ya dogara kacokan da aikin inganta uranium, yana mai nuni da cewa har yanzu man fetur ɗin da tashar samar da wutar lantarki ta Bushehr ke amfani da shi ana shigo da shi ne daga Rasha, ba a cikin gida ake samar da shi ba.

    Yousef Pezeshkian ya kuma ce akwai wasu fasahohi da suka fi muhimmanci ga tsaro da gudanarwar ƙasar, amma ba a ba su kulawar da ta dace ba, yana mai cewa Iran ba ta nuna irin wannan ƙwazo wajen bunƙasa waɗannan fannoni.

  2. Mun samu matsaya da Oman amma ba za mu buɗe Hormuz ba sai Amurka ta cika alƙawurranta - Iran - Iran

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya ce duk da cewa Tehran da Muscat sun cimma matsaya kan samar da wata hanyar wucin gadi ta zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz, Iran ba za ta buɗe mashigar ba har sai Amurka ta cika alkawurran da ta ɗauka.

    Gharibabadi ya jaddada cewa Mashigar Hormuz har yanzu a rufe take, yana mai cewa idan wani jirgin ruwa ya ratsa ta mashigar, sai da izinin Iran.

    A wani labarin da ke da alaƙa da matsin lambar da ake yi wa Tehran, babban bankin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ya sanar da binciken rassan Bankin Masar.

    Matakin ya biyo bayan matakin da Washington ta ɗauka na katse alaƙar bankin da tsarin kuɗi na Amurka, a wani yunkuri na ƙara matsin lamba kan Iran.

  3. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da wannan safiya ta Lahadi.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.