Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta ce ba za ta ƙara wa’adin rijistar masu zaɓe ba, duk da kiraye-kirayen da jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin farar hula suka yi na a ƙara lokaci domin bai wa ƙarin mutane damar yin rajista.
Mataimakin daraktan sashen wayar da kan masu zaɓe da hulɗa da jama’a na INEC, Wilfred Ifogah, ne ya bayyana hakan a wata hira da Gidan talabijin na Channels.
Ya ce, “Dole ne mu kawo ƙarshen aikin rajistar a wannan lokaci. Don haka ga waɗanda ba su samu damar kammala rajistar ba, muna ba su haƙuri, amma a halin yanzu babu abin da za mu iya yi.”
Tun da farko, INEC ta riga ta ƙara wa’adin rajistar da makonni biyu kafin daga bisani ta rufe a ranar Lahadi.
A cewar Ifogah, ƙarin wa’adin da aka bayar tun farko ma ya jefa hukumar cikin ƙarin matsin lamba wajen kammala shirye-shiryen rijistar masu zaɓe kafin babban zaɓen shekara mai zuwa.
Ya ƙara da cewa, “Bisa jadawalin ayyukanmu, muna buƙatar fiye da kwanaki 75 bayan an rufe rijistar domin tattarawa, tantancewa da shirya cikakken rijistar masu zaɓe kafin gudanar da zaɓe.”