INEC ta ƙara wa’adin miƙa sunayen ƴan takarar zaɓen 2027

Asalin hoton, INEC/X
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta ƙara wa’adin da ta bai wa jam’iyyun siyasa domin miƙa sunaye da takardun ’yan takarar da za su fafata a zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Dokoki na 2027.
A cewar hukumar, sabon wa’adin zai ƙare ne da tsakar daren ranar Talata, 14 ga Yuli, maimakon ranar 11 ga Yuli da aka tsara tun farko.
INEC ta bayyana cewa ta ɗauki matakin ne bayan ƙungiyar jam’iyyun siyasa ta IPAC ta buƙaci a ƙara lokaci saboda wasu jam’iyyu ba su kammala saka bayanan ’yan takararsu a shafin hukumar ba.
Hukumar ta buƙaci jam’iyyun siyasa su yi amfani da wannan dama wajen kammala duk bayanan da ake buƙata kafin wa’adin da aka sabunta ya cika.






















