Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya- Asabar, 25-01-2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sassan duniya kai tsaye -Asabar, 25-01-2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Annur Muhammad

  1. Sabbin 'yansanda nawa Najeriya ke buƙatar ɗauka a kowace shekara?

    'Yansanda

    Asalin hoton, NPF.GOV.NG

    Yayin da rudunar ƴansandan Najeriya ta bayyana aniyarta na sake ɗaukar ƴan sanda dubu 30 a kowacce shekara, masu sharhi kan harkokin tsaro a ƙasar na ganin wannan adadi ba zai cike giɓin ƙarancin jami'an da ake da shi ba a ƙasar.

    Masana tsaron na wannan tsokaci ne bayan da babban sufeton ya ce Najeriyar za ta ci gaba da ɗaukar ƴan sanda dubu 30 kowacce shekara.

    Masanan na ganin cewa la'akari da irin ƙalubalen da ake fuskanta daga ɓangaren tsaro a Najeriya, adadin jami'an yan sandan da ake buƙata domin shawo kan matsalar, dole a ruɓanya yawan adadin.

    SP Habibu Shehu Yakawada mai murabus ɗaya ne daga cikin masu wannan ra'ayi, ya ce kawo yanzu adadin 'yansandan Najeriya ba su kai 500,000 ba, kuma idan aka yi la'akari da jihohin da ake da su a Najeriya adadin ya gaza.

  2. Hotunan Falasɗinawan da ke jiran a buɗe musu hanyar arewacin Gaza

    hoto

    Asalin hoton, EPA

    Dubban Falasɗinawa ne suka taru a tsakiyar Gaza, inda suke jiran a buɗe musu hanyar zuwa arewacin yankin.

    Tun da farko Isra'ila ta yi gargaɗin cewa ba za a bai wa 'Yan Gazan damar komawa arewacin yankin ba, har sai an kammala shirin sakin Arbel Yehud wata farar hula da ke cikin waɗanda Hamas ta yi garkuwa da su.

    Ga wasu hotunan falasɗinawa da ke jiran buɗe hanyar al-Rashid da ke kai wa arewacin Gaza, domin komawa gidajensu.

    Hoto

    Asalin hoton, EPA

    Hoto

    Asalin hoton, EPA

    hoto

    Asalin hoton, EPA

  3. Wace ce Arbel Yehud, 'yar Isra'ila da Hamas ke garkuwa da ita da ake magana a kanta?

    Arbel Yehud

    Asalin hoton, The Hostages and Missing Families Forum

    Dubban Falasdinawa ne suka taru a Gaza cikin zaƙuwar a buɗe musu hanya domin su koma arewacin yankin.

    To amma aka jinkirta buɗe hanyar, yayin da tun da farko Isra'ila ta yi gargadin cewa ba za a bai wa 'Falasdinawan damar komawa arewacin Gaza ba, har sai an kammala shirin sakin Arbel Yehud, wata 'yar Isra'ila farar hula.

    Yehud mai shekara 29, lokacin da aka yi garkuwa da ita a Kibbutz Nir Oz a harin ranar 7 ga watan Oktoba da Hamas ta ƙaddamar, an kama ta ne tare da saurayinta, Ariel Cunio ma shekara 27.

    A lokacin harin an kashe ɗan'uwanta, Dolev Yehud, kuma a watan Yunin shekarar da ta gabata ne sojojin Isra'la suka gano gawarsa.

    Tun da farko Isra'ila ta yi tsammanin ganin Yehud, cikin waɗanda za a saki a yau a mataki na biyu na aiwatar da yarjejeniyar musayar fursunoni tsakanin Isra'ila da Hamas, to amma sai a ranar Juma'a Hamas ta tabbatar da cewa ba ta ciki, bayan da ta fitar da sunayen mutanen da za ta saki.

    To amma wasu da suka yi nazarin yarjejeniyar sun fahimci cewa ta tanadi sharadin sakin duka mata fararen hula da ke da rai, kafin sakin mata sojoji.

    To sai dai wata majiyar Hamas ta tabbatar wa BBC cewa ƙungiyar ta shaida wa ƙasar Masar cewa Yehud na nan da ranta, kuma tana cikin mutanen da za a saki a makon gobe.

  4. Isra'ilawan da aka saki yau na cikin 'yanayi mai kyau' - Hukumomin asibiti

    Daraktar Asibitin Beilinson

    Asalin hoton, Reuters

    Daraktar asibitin Beilinson, inda aka kai matan nan huɗu da Hamas ta saki domin a duba lafiyar - ta ce matan waɗanda dukansu sojojin Isra'ila ne, babu wata fargaba a tare da su.

    Dakta Lena Koren Feldman ta ce bayan gwaje-gwajen farko da aka yi wa matan huɗu an gano cewa ba sa cikin wata damuwa.

    Daraktar ta ƙara da cewa asibitin zai ci gaba da ba su duk kulawar da ta dace tare da kula da ƙarfafa musu gwiwa.

    Ta ƙara da cewa kai matan zuwa asibitin domin a duba lafiyarsu alfarma ce ga hukumar asibitin, domin ta taka rawa a warkewar mutanen, tana mai bayyana shi da tsarin warkar da ilarihin al'ummar Isra'ila.

    A yau ne Hamas ta saki matan huɗu a mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin Gaza bayan shafe fiye da wata 15 a hannun Hamas.

  5. Hamas ta ce Arbel Yehud na nan da ranta, kuma za a sake ta a makon gobe

    Yayin da aka yi tsammanin sakin matashiyar nan, Arbel Yehud - da ke cikin mutanen da Hamas ke garkuwa da ita - a yau.

    Wani jami'in Falasɗinawa da ke kusa da Hamas, wanda kuma ke cikin tawagar aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta - ya shaida wa BBC cewa ''Hamas ta sanar da masu shiga tsakanin cewa, Arbel Yehud na nan da ranta, kuma za a sake ta a makon gobe.

    Tun da farko ofishin firaministan Isra'ila ya ce ba za a bari mazauna Gaza su shiga arewacin yankin, har sai an sake ta.

  6. Hamas ta zargi Isra'ila na nuna 'jan ƙafa' a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta

    Hamas ta zargi Isra'ila da ''jan kafa'' a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta bayan da ta ci gaba da rufe babban titin Gaza da zai bai wa Falasɗinawa damar komawa gidajensu a arewaci.

    Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta ce ''ci gaba da rufe titin Al-Rashid domin hana 'yan gudun hijira daga kudanci komawa gidajensu a arewacin Gaza alamu ne na jan ƙafa a yarjejeniyar.

    Hamas ta ce za ta ɗora wa Isra'ila alhakin duk wani abu da ya janyo wargajewar yarjejeniyar, ko tsaiko a wasu matakan aiwatar da yarjejeniyar.

    Ɗaya daga cikin manyan sharuɗan yarjejeniyar shi ne janyewar dakarun Isra'ila daga wuraren masu cunkoson jama'a da kuma Netzarim, wani sansanin soji da ya raba arewacin Gaza daga sauran sassan yankin.

    Sojojin Isra'ilar za su ci gaba da kasancewa a kan iyakokin Gaza, kamar yankin Philadelphi da ke kudanci.

    A yau ne aka kammala mataki na biyu na yarjejeniyar inda Hamas ta saki Isra'ilawa huɗu da take garkuwa da su - waɗanda dukkansu mata ne sojoji - yayin da Isra'ila ta saki Falasdinawa 200 da ke tsare a gidajen yarinta.

  7. Amurka ta dakatar da ba wa ƙasashen waje tallafi

    Donald Trump
    Bayanan hoto, Dakatarwar ba ta shafi samar da kudi ga sojin Isra'ila da Masar ba

    Amurka ta dakatar da ba wa kasashen waje tallafi nan take kamar yadda wata takardar gwamnati da ke kunshe da umarnin wadda aka yi satar fitar da ita ta nuna.

    Sai dai dakatarwar ba ta shafi bayar da taimakon abinci da bayar da kudade ga harkokin sojin Isra'ila da Masar ba, kamar yadda takardar wadda BBC ta tabbatar da ita ta nuna.

    Ma'aikatar harkokin waje ta Amurkar ce ta bayar da umarnin ga jami'ai da ofisoshin jakadancin kasar na waje.

    Matakin ya biyo bayan umarnin da Shugaba Trump ya bayar ne a ranar Litinin na dakatar da bayar da tallafin raya kasashen waje tsawon kwana 90, har zuwa lokacin da za a sake duba tsarin ta yadda zai dace da manufofinsa na kasashen waje.

    Amurka ita ce babbar wadda ta fi ba wa kasashen duniya tallafi inda ta kashe dala biliyan 68 a 2023, kamar yadda alkaluman hukuma suka nuna.

  8. Lokacin da Hamas ke miƙa wa Red Cross sojojin Isra'ila mata huɗu da take garkuwa da su

    Kalli lokacin da Hamas ta miƙa wa Red Cross sojojin Isra'ila mata huɗu da take garkuwa da su a Gaza.

    Sakin nasu wani ɓangare ne na yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin Gaza.

    Ita mai dai Isra'ila ta saki fursunonin Falasɗinawa 200 a yau

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
  9. Hotunan murnar komawar Falasɗinawan da Isra'ila ta saki

    mata

    Asalin hoton, Reuters

    Yayin da hukumomin Isra'ila suka tabbatar da sakin fursunonin Falasɗinawa 200 a yau, tuni wasu daga cikinsu suka koma gida wajen iyalansu.

    Za a bai wa kusan rabin mutanen damar komawa gidajensu a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan.

    Fursunoni saba'in - waɗanda aka samu da manyan laifuka - za a fitar da su zuwa maƙwbatan ƙasashe kamar Qatar da Turkiyya, yayin da za a aika wasu ƙalilan daga cikinsu zuwa Gaza.

    Kusan fursunoni Falasɗinawa 121 da aka saki a makon nan na zaman hukuncin ɗaurin rai da rai ne.

    Ga hotunan wasu Falasdinawa a yayain da suka hadu da iyalansu

    wasu

    Asalin hoton, Reuters

    Fursunonin da suka koma

    Asalin hoton, Reuters

    wasu

    Asalin hoton, Reuters

  10. Isra'ila ta sako Falasɗinawa 200 daga gidan yari

    Jerin motocin Red Cross

    Asalin hoton, Reuters

    Kamar yadda yarjejeniyar dakatar da bude wuta ta tanada tsakanin Isra'ila da Hamas ta musayar fursunoni, bayan da Hamas ta saki rukuni na biyu na 'yan Ira'ila da ta yi garkuwa da su - wasu sojoji mata uku, ita ma Isra'ila a yanzu ta sako Falasdinawa 200 daga cikin wadanda take rike da su a kurkuku.

    A wata sanarwa da hukumomin gidan yari na Isra'ila suka fitar sun ce: ''Bayan kammala dukkanin abubuwan da suka wajaba a gidajen yarin da kuma amincewar hukumomin siyasa an saki dukkanin 'yanta'addan daga gidajen yari na Ofer da Ktziot," kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP da na Reuters, suka ce.

    Ba kamar Falasdinawan da aka saki a makon da ya gabata ba, wadanda yawanci hukuncinsu na zaman gidan yari kadan ne, a wannan karon 121 daga cikin fursunonin suna kan hukuncin rai da rai ne - wasu bisa laifin kisan kai fiye da sau daya da ya hada da kisan farar hula 'yan Isra'ila.

    Shekarun Falasdinawa fursunonin sun bambanta sosai - mafi kankanta da aka saki shi ne mai shekara 16, yayin da mai shekara 69 ya kasance mafi girma a cikinsu.

    Daya daga cikin fursunonin ya shafe shekara 39 a gidan kurkukun Isra'ila, bayan da aka kama shi da farko a 1986.

    Wadanda aka yanke wa hukuncin manyan laifuka mafiya tsanani ba sa cikin wadanda aka saki yau.

    Kusan 70 daga cikinsu za a fitar da su daga Isra'ila ne inda za a bi da su ta Masar zuwa kasashe makwabta da suka hada da Qatar da Turkiyya, kafin a kai su Falasdinu.

  11. Ba zan yarda da raba kan 'yanƙasa ba - Tinubu

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu

    Asalin hoton, Facebook/Bola Ahmed Tinubu

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ce ko alama gwamnatinsa ba za ta lamunta da duk wani abu da zai raba kan al'ummar kasar ba.

    Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya karbi bakuncin jakadiyar kasar Finland a Najeriya, Sanna Selin, a fadarsa da ke Abuja a jiya Juma'a.

    A lokacin ganawar tasu Tinubu ya bayyana farin cikinsa kan yadda hukumomin Finland suka tsare Simon Ekpa, jagoron wani bangare na haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (Ipob), wanda ke zaune a can.

    Tinubu da Simon Ekpa

    Asalin hoton, Presidency/Simon Ekpa/X

    Hukumomin Finland sun kama Ekpa wanda dan Najeriya ne da ke da takardar zama dan kasar ta Turai sakamakon abubuwan da yake yi daga can da ke janyo ce-ce-ku-ce tare da haddasa tashin hankali a yankin kudu maso gabashin Najeriya.

    Wannan shi ne karon farko da shugaban na Najeriya ya yi magana a kan Ekpa, tun bayan kama dantawayen a shekarar da ta wuce a kan zarin ta'addanci.

    A nata bangaren jakadiyar Finland din ta bayyana cewa Simon Ekpa na haifar da cikas a dangantaka tsakanin kasashen biyu.

    Kuma a yanzu bayan tsare shi alaka ta ci gaba da wanzuwa da kyau tsakanin kasashen.

    Hukumomin Finland sun kama Ekpa wanda dan Najeriya ne da ke da takardar zama dan kasar ta Turai sakamakon abubuwan da yake yi daga can da ke janyo ce-ce-ku-ce tare da haddasa tashin hankali a yankin kudu maso gabashin Najeriya.

    Wannan shi ne karon farko da shugaban na Najeriya ya yi magana a kan Ekpa, tun bayan kama dantawayen a shekarar da ta wuce a kan zarin ta'addanci.

    A nata bangaren jakadiyar Finland din ta bayyana cewa Simon Ekpa na haifar da cikas a dangantaka tsakanin kasashen biyu.

    Kuma a yanzu bayan tsare shi alaka ta ci gaba da wanzuwa da kyau tsakanin kasashen.

  12. Likitoci sun janye yajin aiki a Abuja

    Likitoci a zaune

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta janye yajin aikin gargadi na kwana uku da mambobinta suka shiga a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.

    A wata sanarwa da shugaban kungiyar, Dr. George Ebong ya fitar a jiya Juma'a ya ce sun dakatar da yajin aikin ne bayan da ministan babban birnin Nyesome Wike ya shiga tsakani, inda aka biya musu da dama daga cikin bukatunsu.

    A ranar Laraba ne kungiyar ta tsunduma yajin aikin a kan rashin biya musu wasu bukatu da suka hada da bashin albashi da kuma kudaden alawus-alawus da sauransu.

    A sanarwar janye yajin aikin, dr Ebong ya ce tuni wasu daga cikin likitocin suka fara samun kudaden bashin da suke bi na karin albashi da ba a biya su ba na wata shida,

    Shugaban ya ce bayan da ministan ya sa baki a kan bukatun nasu har aka fara share musu hawaye, likitocin sun koma bakin aiki a yau Asabar 25 ga watan Janairu, 2025.

  13. 'Yantawayen Jamhuriyar Kongo sun kashe gwamna

    Mutane a kwaura

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Jama'a na ta guduwa daga yankunan da 'yantawayen ke kamawa

    'Yantawayen kungiyar M23 na Jamhuriyar Dumukuradiyyar Kongo da Rwanda ke marawa baya sun kashe wani gwamnan soji yayin da suka durfafi gabashin kasar.

    A wata sanarwa suka fitar jiya Juma'a mayakan sun ce sun harbe gwamnan jihar North Kivu, Manjo Janar Peter Cirimwami a lokacin da ya ziyarci fagen daga a shekaran jiya Alhamis.

    Daga can aka dauke shi a jirgin sama zuwa babban birnin kasar kinshasa domin a fita da shi waje a yi masa magani amma rai ya yi halinsa kamar yadda kakakin rundunar sojin kasar Janar Sylvain Eken ya tabbatar.

    Fada tsakanin sojojin kasar ta Kongo da mayakan kungiyar ta M23 ya tsananta tun shigowar wannan shekara inda 'yantawayen ke ci gaba da kama yankuna fiye da a baya.

    Sama da mutum 400,000 ne suka tsere daga muhallinsu people have fled their homes sinctyayin da 'yantawayen ke durfafar birnin Goma in ji wani rahoto na Majalisar Dinkin Duniya.

    Sama da farar hula 200 aka kashe a yankunan da 'yantawayen suka kama in ji shugabannin yankunan ranar Alhamis.

    Ana yi wa daruruwan mutane magani a asibitocin birnin na Goma.

  14. Sojoji mata huɗu da Hamas ta saki sun koma Isra'ila

    Mata sojin Israila

    Asalin hoton, OTHERS

    Sojojin Isra'ila mata hudu da Hamas ta saki sun koma Isra'ila kamar yadda rundunar sojin kasar (IDF) ta tabbatar.

    Sojojin hudu wadanda su ne Daniela Gilboa, da Liri Elbag, da Naama Levy da kuma Karina Ariev, za su kasance a cibiyar da aka tanadar ta musamman wajen ajiye wadanda aka saki kafin daga bisani su gana da iyayensu.

    Tun da farko kafin sakin nasu mayakan Hamas sun taru a Dandalin Falasdinu da ke Gaza, domin danka wadanda za su saki ga kungiyar agaji ta Red Cross.

    Wannan shi ne kashi na biyu na Isra'ilawa da Hamas ta yi garkuwa da su da ta saki bayan cimma yarjejeniyar dakatar da bude wuta tsakaninta da Isra'ila.

    Ita ma Isra'ila za ta saka wa Hamas da sakin Falasdinawa wajen 200 da take rike da su a gidajen yarinta.

    Ana sa ran Hamas za ta bayar da bayani a kan wasu Isra'ilawan 26 da za ta sake saki a makonnin da ke tafe.

    Sojojin Isra'ila za su janye daga muhimman wurare a Gaza, domin Falasdinawa da suka yi gudun hijira su koma arewacin birnin.

  15. Buɗewa

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafin da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, muna muku maraba a wannan rana ta Asabar 25 ga Janairun 2025.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu da sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo.

    Ku kasance tare da mu.