Na yi amannar Iran za ta amince da yarjejeniyar nukiliya - Trump
Shugaba Trump ya ce ya yi amanna Iran na son a cimma yarjejeniya akan shirinta na Nukiliya. Ya yi kalaman ne a yammacin ranar da za a fara zagaye na biyu na tattaunawar da ake tsakanin wakilan Amurka da na Iran a Geneva wanda Oman ke shiga tsakani.
Wakilin BBC ya ce, Mr Trump ya ce ba ya tunanin Iran na son abin da zai biyo baya idan har ta ki yarda ta kulla yarjejeniyar sannan kuma ya yi amanna Iran din na son a cimma yarjejeniyar.
A nata ɓangaren ma'aikatar harkokin wajen Iran ta bakin mai magana da yawunta, ya ce yanzu Amurka ta fi nuna da gaske take musamman kan batun matsayarta kan batun nukiliya .