Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/06/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/06/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Babangida

  1. Iran ta kashe mutumin da aka kama yana yi wa Isra'ila leƙen asiri

    Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga mutumin da aka kama yana yi wa Isra'ila leƙen asiri.

    Hukuma ta ce an kama Esmail Fekri a shekarar 2023, kuma yana ƙoƙarin miƙa wa Isra'ila bayanan sirri ne don samun kuɗi.

    Wannan ne karo na uku a baya-baya nan da Iran ke aiwatar da hukuncin kisa saboda zargin leƙen asiri ga Isra’ila.

    A ranar Lahadi, Isra’ila ta ce ta kama wasu ‘yan ƙasa biyu da ake zargin suna aiki da hukumar leƙen asirin Iran.

    Babban alƙalin Iran, Gholamhossein Mohseni Ejei, ya bayyana a ranar Litinin cewa, la'akari da yanayin “yaƙi” da suke ciki, dole ne a gudanar da shari’o’i ga waɗanda ake zargin suna aiki da Isra’ila cikin hanzari.

  2. Hotunan da ke nuna ɓarnar da harin Isra'ila ta haddasa a Iran

    Ga wasu hotuna da suka fito daga birnin Tel Aviv da ke nuna ɓarnar da harin Isra'ila ta haddasa a Iran da safiyar Litinin, da kuma yadda jami’an ceto ke bincike domin gano gawwarwaki da kuma waɗanda suka rayu a harin.

  3. Israila ta ce ta kankane sararin samaniyan Iran

    Wani mai magana da yawun rundunar sojan Isra’ila ya bayyana cewa Isra’ila ta kankane sararin samaniya a saman birnin Tehran na Iran.

    A wani taron manema labarai, Birgediya Janar Effie Defrin ya ce: “Mun lalata fiye da kashi ɗaya bisa uku na makaman harba roƙa na ƙasa-zuwa-ƙasa da gwamnatin Iran ke da su.”

  4. Kalli yadda makaman Iran suka faɗa kan biranen Isra'ila

    An kwashe dare na uku ana musayar wuta tsakanin Iran da Ira'ila, inda Iran ta riƙe cilla makamai masu linzami zuwa fadin Isra'ila.

    Bidiyo ya nuna yadda irin wadannan makamai suka faɗa kan biranen Tel Aviv da kuma Haifa.

  5. 'Dole Amurka ta yi Allah-wadai da Isra'ila idan tana so a yi tattaunawar nukiliya'

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghai ya bayyana cewa bayan soke tattaunawar nukiliya tsakanin Amurka da Iran da aka shirya yi jiya Lahadi, dole ne Amurka ta fito fili ta yi Allah-wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa kan Iran kafin a ci gaba da tattaunawar.

    Esmail Baghai ya sake jaddada cewa tattaunawar nukiliya “ba ta da ma’ana” a halin da ake ciki yanzu, yana mai cewa Amurka tana da hannu a hare-haren da Isra’ila ke kai wa Iran.

    Haka kuma, ya ce idan majalisar dokokin Iran ta yanke shawarar janyewa daga yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliya (NPT), wannan hukunci zai zama doka ce da dole ne a aiwatar da ita.

    Iran ta kafe cewa shirinta na nukiliya na zaman lafiya ne, sai dai Isra’ila na musanta wannan ikirari.

  6. Isra'ila ta ce hare-haren Iran sun kashe mutum takwas a daren Litinin

    Isra'ila ta ce an kashe mata mutum takwas a dare na uku na hare-haren da Iran ke kaddamarwa kan unguwanni al'umma a biranen Tel Aviv da Haifa da ma fadin kasar.

    Hakan ya kawo yawan mutanen da hare-haren Iran din suka kashe zuwa 24.

    Jami'an lafiya a kasar ta Isra'ila sun ce kimanin mutum 300 aka kwantar a asibiti sanadiyyar raunukan da suka samu.

    Ma'aikatar sojin Isra'ila ta ce jiragen yakinta sun kai hari kan shalkwatar Dakarun juyin-juya hali na Iran da ke Tehran, babban birnin Iran.

    Haka nan tun farko rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kai farmaki kan cibiyoyin harba makamai da Iran ke amfani da su da ke tsakiyar kasar.

    Iran ta ce an kashe mata mutum sama da 200 tun bayan harin da Isra'ila ta kaddamar a kanta da asubahin Juma'ar makon da ya gabata.

  7. Amurka na shirin faɗaɗa hana ƙarin ƙasashen Afrika 25 shiga ƙasar

    Gwamnatin Trump na shirin faɗaɗa hana ƙarin ƙasashen Afrika 25 tafiya zuwa Amurka.

    Wannan mataki na zuwa ne sakamakon damuwa da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta nuna game da matsalolin tsaro da rashin haɗin kai wajen mayar da ‘yan ƙasa, da kuma yawaitar wuce wa’adin izinin zama a cikin ƙasashen da ake nazari a kansu a cikin kwanaki 60 masu zuwa.

    Daga cikin ƙasashen Afirka da ake yi wa cikakken sa ido akwai Angola da Benin da Burkina Faso da Cape Verde da Kamaru da Côte d'Ivoire da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da Djibouti da Habasha da Masar da kuma Gabon.

    Sauran ƙasashen sun haɗa da Gambia da Ghana da Liberia da Malawi da Moritaniya da Nijar da Najeriya da São Tomé da Príncipe da Senegal da Sudan ta Kudu da Tanzaniya da Uganda da Zambia, da kuma Zimbabwe.

    Idan aka aiwatar da wannan shiri, zai kasance shine shirin mafi girma da Amurka ta yi na haramta wa ƙasashen Afrika shiga ƙasar idan aka yi la'akari da ƙasashe Afrika 10 na farko da haramcin ya shafa.

    Wannan sabon shirin zai shafi kusan kashi biyu bisa uku na ƙasashen Afirka wajen tafiya zuwa Amurka.

  8. China ta buƙaci Isra’ila da Iran su rage tashin hankali

    China ta sake yin kira ga Isra’ila da Iran da su ɗauki matakai na rage tashin hankali yayin da hare-hare ke ci gaba daga bangarorin biyu.

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen China, Guo Jiakun, ya ce, “Muna kira ga dukkan ɓangarorin biyu da su ɗauki matakan rage tashin hankali nan take, su hana yankin fada wa cikin matsaloli masu tsanani."

    ya kuma buƙaci su samar da yanayi na komawa kan hanyar warware matsaloli ta hanyar tattaunawa da shawarwari.”

    Maganganun nasa sun biyo bayan wata sanarwa da wani mai magana da yawun ma’aikatar a ranar Lahadi ya yi, inda ya ce “China tana shirye ta taka rawa mai amfani a tsarin rage tashin hankalin da ke faruwa a Iran da Isra'ila.”

  9. Masu aikin ceto a Isra'ila na neman mutanen da suka maƙale a ɓaraguzai bayan harin Iran

    Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba da neman mutanen da suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine a birnin Tel Aviv.

    An ji ƙarar fashewar manya-manyan abubuwa a wasu biranen Isra'ila ciki har da Tel Aviv da Jerusalem, yayin da Iran ta ci gaba da harba makamai masu linzami cikin dare zuwa Isra'ila.

    Hotunan da aka wallafa a Intanet sun nuna yadda gine-gine suka ruguje.

    Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Isra'ila ta ce mutum biyar ne suka mutu sannan wasu sama da casa'in suka jikkata, a hare-haren na cikin dare.

    Ƙasashen Isra'ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta cikin dare a yayin da aka shiga kwana na huɗu a rikici tsakanin kashen biyu.

    Hare-haren na Iran sun kuma shafin birnin Haifa da ke arewacin ƙasar, wanda ya kasance cibiyar babbar tashar jirgin ruwa da matatar matar mai.

    Tun da farko Iran ta tabbatar da cewa an kashe shugaban sashen leƙen asiri na rundunar dakarun ƙare juyin juya hali ta ƙasar da mataimakinsa da wani kwamanda a wani harin da Isra'ila ta kai birnin Tehran.

    Ma'aikatar lafiyar Iran ta ce aƙalla mutum 224 ne suka mutu tun bayan aka fara kai mata hare-haren.

    A nata ɓangare Isra'ila ta ce kawo yanzu an kashe mutum 19, tun bayan fara hare-haren.

  10. Hukumar kula da makamashin nukiliya za ta yi taro kan hare-haren cibiyoyin nukiliyar Iran

    Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya (IAEA) ta shirya wani taro na musamman a yau inda za a tattauna hare-haren da Isra'ila ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran.

    Majalisar gudanarwar hukumar za ta gana ne sakamakon wata buƙata ta musaman daga Rasha.

    Shugaban hukumar ta IAEA, Rafael Grossi, ya shaida wa kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya a ranar Juma'a cewa Isra'ila ta kai hari kan cibiyoyin nukiliyar Iran da ke Isfahan da Fordow, da kuma babbar cibiyar sarrafa Uranium ta kasar da ke Natanz.

    An kashe masana kimiyya shida da suka haɗa da ƙwararru kan makamashin nukiliya guda biyu a hare-haren.

  11. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkanmu da safiyar wanann rana ta Litinin da Hausawa ke yi wa kirari da ''Mande tushen aiki ko da Nasara na tsaronki''.

    Aisha Babangida ke fatan jagorantar wannan shafi a daidai wannan lokaci - bisa kulawar Ibrahim Haruna Kakangi - domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Kuna iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.