Wike ya gargaɗi masu haɗaka su daina amfani da ƴan Najeriya don cimma manufofinsu
Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya gargaɗi masu shiga sabuwar haɗaka da aka kafa, da su daina amfani da ƴan Najeriya don cimma manufofinsu.
Wike ya bayyana haka ne ranar Alhamis lokacin da yake tattaunawa da ƴan jarida a gidansa da ke Abuja.
A cewarsa, sabuwar haɗaka da wasu fitattun ƴan siyasa suka shiga ta hanyar amfani da jam'iyyar ADC, sun yi ta ba don buƙatun ƴan Najeriya ba, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.
"Saboda kana fushi da wani, sai ka ce ƴan Najeriya sun fusata sannan ka ja-gaba wajen shiga haɗaka. Ya kamata mu ɗauki batutuwan Najeriya da muhimmanci.
"Ina kalubalantar dukkan waɗanda suka shiga haɗakar da su nuna irin ci gaba da suka kawo lokacin da suke kan mulki. Me suka yi wa ƙasar," in ji Wike.