Rundunar ƴansanda ta tabbatar da kashe jami'anta 10 a artabu da ƴanbindiga a Kebbi

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar ƴansandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami'anta 10 a wani artabu da ƴanbindiga a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Rundunar ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:25 na safiyar Litinin 10 ga watan Agusta, a yankin Rafin Makuku da ke ƙaramar hukumar Sakaba.
A sanarwar da kakakin rundunar na ƙasa CSP Ani Iniedu ya fitar, ya ce jami'anta sun tare ƴanbindigar ɗauke da muggan makamai ne yayin da suke ƙoƙarin wucewa daga jihar Zamfara zuwa Kebbi, inda suka yi musayar wuta.
Rundunar ta ce an kashe aƙalla ƴanbindiga 17 tare da lalata babura huɗu na maharan.
Sai dai jami'an ƴansanda 10 sun rasa rayukansu a artabun, yayin da wasu biyu suka samu raunuka inda a yanzu suke samun kulawa.
Rundunar ta kuma ce wasu fararen hula biyu sun mutu a yayin musayar wutar.




























