Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Labaran wasannin BBC Hausa

Wannan shafi na kawo muku labaran wasanni da kasuwar 'yan wasanni ta duniya daga nan BBC Hausa daga 24 zuwa 30 ga watan Agusta

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Buhari Fagge

  1. Rayuwar Delap a kwallon ƙafa

    Ga yadda Liam Delap ya taka rawa a matakin manyan 'yan wasa a cikin shekaru hudu da suka gabata:

    • 2025-26 (Chelsea) Wasanni: 28 a Premier League Kwallaye: 1 Taimaka wa kwallaye 1
    • 2024-25 (Ipswich Town) Wasanni: 37 a Premier League Kwallaye: 12 Assists: 2
    • 2023-24 (Hull City) Wasanni: 31 a Championship Kwallaye: 8 Assists: 2
    • 2022-23 (Stoke City) Wasanni: 37 a Championship Kwallaye: 4 Assists: 0

    A jumlace ya buga wasanni 133 inda ya ci kwallaye 25 ya kuma taimaka aka ci 5.

    Kididdigar ta nuna cewa Delap ya fi yin fice a kakar 2024-25 tare da Ipswich Town, inda ya zura kwallaye 12 a Premier League. Sai dai bayan komawarsa Chelsea, ya sha wahala wajen samun kwallaye, inda ya ci ɗaya kacal tare da bayar da ɗaya a wasanni 28 na gasar. Wannan ne ya sa ake rade-radin cewa Nottingham Forest na son daukarsa domin ya samu damar buga wasa akai-akai da kuma farfado da bajintarsa.

  2. 'Yan wasan da Manchester City ta sayar

    Manchester City ta yi bankwana da wasu fitattun 'yan wasa a wannan bazarar, inda kudin da ta samu daga sayar da 'yan wasa ya kai fam miliyan 251.5.

    'Yan wasan da suka bar Manchester City

    • Savinho zuwa Tottenham Hotspur – £75m
    • Rodri zuwa Barcelona – £65m
    • Tijjani Reijnders zuwa Al-Qadsiah – £52m
    • James Trafford zuwa Leeds United – £45m
    • Nathan Aké zuwa Fenerbahçe – £8.5m
    • Reigan Heskey zuwa Cologne – £6m
    • Bernardo Silva zuwa Real Madrid – Kyauta (Free Transfer)
    • John Stones zuwa Inter Milan – Kyauta (Free Transfer)

    Jimillar kudaden da City ta samu fam miliyan 251.5m daga sayar da 'yan wasa shida da aka biya kudinsu.

    Wannan kudin ne ya taimaka wa kungiyar wajen daukar sababbin 'yan wasa, ciki har da Ayyoub Bouaddi (£85.6m) da sauran sabbin masu zuwa a bazarar nan.

  3. Ana tuhumar Sterling da tuƙin ganganci

    Raheem Sterling zai gurfana a gaban kotu a wata mai zuwa domin fuskantar tuhume-tuhume na tukin ganganci da kuma mallakar iskar nitrous oxide domin shakar da ba bisa ƙa'ida ba, bayan hadarin mota da ya yi a watan Mayu.

    Tsohon dan wasan gefe na Ingila, wanda ya koma taka leda a kungiyar Feyenoord ta Holland, ya yi hadari da motarsa kirar Lamborghini inda ta bugi katanga a babbar hanyar M3 da ke Hampshire da safiyar Alhamis, 28 ga Mayu, 2026.

    An kama Sterling mai shekaru 31 bayan hadarin, amma daga bisani aka sake shi a kan beli yayin da ake ci gaba da bincike.

    Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Hampshire da Isle of Wight ya ce “Wani direba zai gurfana a gaban kotu a wata mai zuwa domin fuskantar tuhume-tuhume bayan wani hadari da ya faru a kan babbar hanyar M3.

    Raheem Sterling, mai shekaru 31 daga Berkshire, an tuhume shi da laifuka kamar haka: Tukin ganganci, Mallakar iskar nitrous oxide domin shakar ba bisa ƙa'ida ba,Kin bayar da samfurin gwaji.

    A halin yanzu, Sterling zai bayyana a gaban kotu domin amsa wadannan tuhume-tuhume, yayin da ake jiran ci gaban shari’ar.

  4. Newcastle ta amince ta sayi Gonzalez kan £52m daga City

    Newcastle United ta cimma yarjejeniya da Manchester City kan sayen dan wasan tsakiya Nico Gonzalez kan kudi fam miliyan 52.

    Newcastle ta mayar da hankali kan sayen ‘yan wasa daga kasashen Turai a wannan kasuwar saye da sayarwa, amma shugabannin kulob din sun fahimci bukatar kara gogaggun ‘yan wasan da suka saba da Premier League bayan tafiyar manyan ‘yan wasan kungiyar kamar Bruno Guimaraes, Sandro Tonali, Anthony Gordon da Kieran Trippier a ‘yan watannin nan.

    Nico Gonzalez, mai shekara 24, ya shafe kakar wasa daya da rabi kacal a Premier League bayan komawarsa Manchester City daga Porto.

    Duk da haka, yana cikin tsarin shekarun ‘yan wasan da Newcastle ke nema, wato matasa masu damar ci gaba da bunkasa karkashin jagorancin koci Matthias Jaissle.

    A baya, Gonzalez ya bayyana cewa bai son barin Etihad Stadium, amma daga baya Manchester City ta amince da sayen dan wasan Lille Ayyoub Bouaddi kan fam miliyan 85.6. Tuni kuma City ta dauki Elliot Anderson daga Nottingham Forest a wani gagarumin ciniki na fam miliyan 116.

    A karshen makon da ya gabata, Gonzalez ya kasance a benci ba tare da buga wasa ba yayin da Manchester City ta doke Bournemouth da ci 2-1 bayan ta farke daga baya a wasan farko na Premier League karkashin sabon koci Enzo Maresca.

    Idan aka kammala cinikin, Gonzalez zai zama dan wasan tsakiya na hudu da zai bar Manchester City a wannan bazarar bayan Bernardo Silva, Rodri da Tijjani Reijnders.

  5. Man City ta kammala ɗaukar Bouaddi daga Lille

    Manchester City ta kammala daukar dan wasan tsakiya Ayyoub Bouaddi daga Lille kan kudi fam miliyan 85.6, lamarin da ya sa dan wasan na Morocco mai shekara 18 ya zama matashin dan wasa mafi tsada da aka taba saya a Premier.

    Bouaddi ya sanya hannu kan kwantiragin shekara biyar da City, sai dai ana jiran kammala takardun izinin kasa da kasa. City za ta biya fam miliyan 81.4 nan take, sannan akwai karin fam miliyan 4.2 a matsayin wasu kudaden kari.

    Kungiyar Enzo Maresca ta dauki matakin sayen Bouaddi ne bayan ta sayar da ‘yan wasan tsakiya Rodri zuwa Barcelona kan fam miliyan 65, da kuma Tijjani Reijnders zuwa Al-Qadsiah kan fam miliyan 52.

    Bouaddi ya burge mutane da dama a gasar cin kofin duniya ta bana, inda ya fara wasa a wasanni biyar daga cikin shida da Morocco ta buga a hanyarta ta zuwa wasan daf da na kusa da na karshe. Haka kuma ya zama daya daga cikin muhimman ‘yan wasan Lille a gasar Ligue 1 ta Faransa.

    Bouaddi ya buga wasanni 96 a Lille tun bayan da ya fara taka leda a kungiyar ta farko a shekarar 2023, kuma ya taimaka musu wajen kammala kakar da ta gabata a matsayi na uku a gasar Ligue 1.

  6. Nottingham Forest na son sayen Delap daga Chelsea

    Kungiyar Nottingham Forest na aiki kan yarjejeniya domin daukar ɗan wasan gaba na Chelsea, Liam Delap.

    Chelsea ta bayyana cewa a shirye take ta sayar da ɗan wasan mai shekaru 23 kan kuɗin fam miliyan 50, kuma a halin yanzu yana atisaye ne daban da tawagar farko ta ƙungiyar.

    Har yanzu ba a tabbatar ko tattaunawar da ake yi ta shafi saye na dindindin ko kuma aron ɗan wasan ba, amma an san cewa Nottingham Forest da Chelsea suna da kyakkyawar alaƙar aiki tsakaninsu.

    Ba a fito da Delap ba cikin tawagar Chelsea da ta buga wasan Premier League da Fulham a ranar Litinin, sannan a makon da ya gabata ya rasa rigarsa mai lamba 9 inda aka bai wa takwaransa na gaba Joao Pedro.

    Yiwuwar barinsa Stamford Bridge na zuwa ne bayan fiye da shekara guda kacal da komawarsa Chelsea daga Ipswich Town kan kuɗin fam miliyan 30.

    Sai dai kakar wasan da ta gabata ba ta yi masa daɗi ba, domin ya kammala ta ne da ƙwallo ɗaya kacal a Premier, sakamakon raunukan kafaɗa da kuma tsokar baya cinyarsa da suka hana shi buga wasanni akai-akai.

  7. 'Yan wasan da suka zo Man Utd

    Ga sabbin 'yan wasan da Manchester United ta dauko a wannan bazarar:

    • Kit Margetson (Swansea City zuwa Manchester United) – Ba a bayyana kuɗin cinikin ba
    • Andrey Santos (Chelsea zuwa Manchester United) – £48m
    • Karl Darlow (Leeds United zuwa Manchester United) – Kyauta
    • Youri Tielemans (Aston Villa zuwa Manchester United) – £35m
    • Cristian Orozco (Fortaleza CEIF zuwa Manchester United) – Ba a bayyana kuɗin cinikin ba
    • Tynan Thompson (Tottenham Hotspur zuwa Manchester United) – Har zuwa £8m

    Idan aka haɗa kuɗaɗen da aka bayyana a hukumance, Manchester United ta kashe aƙalla fam miliyan 91 wajen sayen sabbin 'yan wasa a wannan bazarar, ba tare da ƙididdige kuɗin Kit Margetson da Cristian Orozco ba.

    Haka kuma, idan aka kammala cinikin Carlos Baleba daga Brighton kan kuɗin da zai kai £70m, jimillar kuɗin da United za ta kashe a kasuwar bana za ta haura fam miliyan 160.

    Zuwan Andrey Santos, Youri Tielemans, da kuma yiwuwar zuwan Carlos Baleba na nuna cewa Manchester United ta mayar da hankali sosai wajen ƙarfafa tsakiyar fili domin ƙara inganta ƙungiyar kafin sabuwar kakar wasa ta fara nisa.

  8. Ko Baleba zai iya jurewa matsin lambar United?

    Ga wasu daga cikin ra'ayoyin ku kan yunƙurin Manchester United na ɗauko ɗan wasan tsakiyar Brighton, Carlos Baleba, bayan sun yi ƙoƙarin sayensa tun bara:

    Dave: "Wannan dai kamar yanke shawara ne a mintinan ƙarshe! Na san an dade ana magana a kai kusan shekara guda, amma a cikin wannan shekarar bai yi wani abin a zo a gani ba. A ganina zaɓi ne mara kyau. Myles Lewis-Skelly ya fi Baleba a kusan dukkan fannoni, ko na ƙwallo ko na kuɗi. Kuma mafi muhimmanci, yana cikin ƙoshin lafiya. Baleba bai kai Andrey Santos ba, amma kuma ya fi shi tsada."

    Howard: "Ina farin ciki da wannan. Muna buƙatar ƙarfin tsakiya kuma zai iya samar mana da hakan. Haka kuma yana son zuwa Manchester United, wanda abu ne mai kyau. Bai kamata mu mayar da hankali sosai kan rashin kyakkyawan kakar wasansa ta bara ba, domin hankalinsa ya rabu ne sakamakon batun canjin kulob. Ina ganin zai yi mana amfani sosai. Mu yi fatan yarjejeniyar ta tabbata, domin muna buƙatar ƙwararren ɗan wasan tsaron tsakiya irinsa."

    Thomas: "Akwai 'yan wasa masu hazaka sosai da suka gaza a Manchester United, sannan akwai wasu da ba a yi musu wani tsammani ba amma suka yi fice. Abin da muke buƙata shi ne 'yan wasa masu ƙwarin hali da tunanin zakara. Idan yana da wannan, to yana da cikakken goyon bayana."

    Mark: "Babban abin da ke damuna game da Baleba shi ne ko zai iya jure matsin lambar da ke Manchester United. Wasansa ya ragu sosai a kakar da ta gabata. Idan hakan ya faru ne saboda canjin da bai tabbata ba, to abin zai sa a yi tambaya kan ƙarfin halinsa. Idan kuma ba haka ba ne, to dole a tambayi dalilin da ya sa hakan ya faru da kuma ko zai iya dawo wa irin wannan bajintar."

    Coops: "Na yi matuƙar mamakin wannan labari. Wani matsakaicin ɗan wasan tsakiya ne kuma, alhali muna matuƙar buƙatar sake gina tsaronmu. Maxence Lacroix, Ezri Konsa da Jan Paul van Hecke duk sun koma ƙungiyoyin hamayyarmu. Wata kasuwar saye da sayarwa mara kyau ce, duk da alkawuran da aka yi mana, kamar yadda aka saba!"

  9. Wane ne Bouaddi?

    Ayyoub Bouaddi ya burge mutane da dama a gasar Kofin Duniya ta bana, inda ya fara wasa a wasanni biyar cikin shida da Morocco ta buga har ta kai zagayen kwata fainal. Tun da farko, ya fara jan hankali sosai a duniya bayan rawar da ya taka wajen taimakawa Lille ta doke Real Madrid a gasar Champions League a shekarar 2024.

    Bouaddi na taka rawa a matsayin ɗan wasan tsakiya mai jan ragamar wasa daga baya, wato wanda ke tsara kai hare-hare da rarraba ƙwallaye daga zurfin fili. Salon wasansa zai dace sosai da Elliot Anderson, wanda kuma ke iya taka rawa a matsayin ɗan wasan tsakiya mai kai-komo, baya ga matsayin lamba shida da yake bugawa Ingila.

    Bouaddi ya fara buga wa babbar ƙungiyar Lille wasa ne a watan Oktoban 2023, kwanaki uku kacal bayan cika shekaru 16 da haihuwa. Tun daga lokacin ya buga wasanni 88 ga Lille, sannan ya taimaka wa ƙungiyar ta kammala kakar wasan Ligue 1 da ta wuce a matsayi na uku.

    Haka kuma, ya karya tarihin da fitaccen tsohon ɗan wasan Lille, Eden Hazard, ya kafa, bayan ya kai wasanni 50 a gasar lig ta Faransa yana da shekaru 18 kacal.

  10. Man Utd ta amince ta biya £70m kan Baleba na Brighton

    Manchester United ta cimma yarjejeniya da Brighton kan cinikin ɗan wasan tsakiya Carlos Baleba a kuɗin da zai iya kaiwa fam miliyan 70.

    Kungiyoyin biyu sun samu nasarar cimma matsaya a tattaunawarsu a daren Juma'a, lamarin da ya bai wa ɗan wasan mai shekaru 22 damar zuwa domin gwajin lafiya tare da Manchester United a wannan karshen mako.

    United ta mayar da hankalinta kan ɗan wasan na ƙasar Kamaru ne a wannan makon bayan ta yanke shawarar ƙara ƙarfafa tsakiyarta, biyo bayan zuwan Andrey Santos daga Chelsea da kuma Youri Tielemans daga Aston Villa.

    Manchester United za ta biya fam miliyan 65 da farko, sannan akwai yiwuwar ƙarin fam miliyan 5 idan wasu sharuɗɗa sun cika. Haka kuma, Brighton ta saka sharadin samun wani kaso daga kuɗin da za a sayar da Baleba a nan gaba.

    Baleba, wanda ya koma Brighton daga Lille a shekarar 2023, yana jinya a halin yanzu sakamakon raunin idon sawu da ya samu yayin wasannin shirye-shiryen fara kakar wasa da ƙungiyar ta yi a ƙasar Austria.

    Idan aka kammala cinikin, jimillar kuɗin da Manchester United ta kashe wajen sayen 'yan wasa a wannan bazarar za ta kai fam miliyan 153.

    Sai dai kuma, wannan ciniki na nufin United ta samu rangwame mai yawa idan aka kwatanta da kuɗin da Brighton ke nema yayin da ake gab da rufe kasuwar musayar 'yan wasa ta shekarar 2025.

  11. Waɗanda suka bar Man City

    Ga 'yan wasan da Manchester City ta sayar ko kuma suka bar ƙungiyar zuwa yanzu a wannan bazarar:

    • Tijjani Reijnders (Manchester City zuwa Al-Qadsiah) – £52m
    • Rodri (Manchester City zuwa Barcelona) – kusan £65m
    • James Trafford (Manchester City zuwa Leeds United) – ba a bayyana kuɗin cinikin ba
    • John Stones (Manchester City zuwa Inter Milan) – kyauta
    • Manuel Akanji (Manchester City zuwa Inter Milan) – £13m
    • Nathan Aké (Manchester City zuwa Fenerbahce) – £7m
    • Bernardo Silva (Manchester City zuwa Real Madrid) – kyauta
    • Savinho (Manchester City zuwa Tottenham Hotspur) – £75m

    Wadannan sauye-sauye na nuna babban canji a tawagar Manchester City, inda fitattun 'yan wasa irin su Rodri, Bernardo Silva, John Stones da Savinho suka bar kungiyar.

    Sai dai mafi daukar hankali shi ne cinikin Savinho zuwa Tottenham kan fam miliyan 75, da kuma komawar Rodri Barcelona a kan kudin da ake hasashen ya kai kusan fam miliyan 65.

    Idan aka hada kudaden da aka bayyana a hukumance, Manchester City ta samu akalla fam miliyan 212 daga sayar da 'yan wasa a wannan bazarar, ba tare da lissafa kudin James Trafford da sauran yiwuwar kari da ke cikin wasu yarjejeniyoyi ba.

  12. Man City ta amince ta biya £81.4 kan Bouaddi

    Manchester City sun cimma yarjejeniya ta farko mai darajar Yuro miliyan 100 (£85.6m) domin daukar matashin ɗan wasan tsakiya na Lille, Ayyoub Bouaddi mai shekaru 18.

    BBC Sport ta ruwaito a farkon wannan makon cewa kungiyoyin biyu na tattaunawa a mataki na karshe kan cinikin ɗan wasan ƙasar Morocco zuwa City.

    Yanzu an cimma matsaya kan yarjejeniyar da za ta kai Bouaddi zuwa kungiyar da Enzo Maresca ke jagoranta, inda Lille ta amince da karɓar £81.4m a matsayin kuɗin farko, tare da ƙarin £4.2m na kari idan wasu sharuɗɗa sun cika.

    Bayan da City ta sayar da 'yan wasan tsakiya Rodri zuwa Barcelona kan £65m da kuma Tijjani Reijnders zuwa kungiyar Al-Qadsiah ta Saudiyya kan £52m, kungiyar ta mayar da hankali wajen ƙarfafa tsakiyar fili.

    Har yanzu City na sha'awar ɗan wasan Chelsea Enzo Fernandez, amma har yanzu ba a san ko za a iya cimma yarjejeniya ba.

    Tuni kuma kungiyar ta kara ɗan wasan Ingila Elliot Anderson daga Nottingham Forest kan £116m.

  13. Sabbin 'yan wasan City

    Ga sababbin 'yan wasan da Manchester City ta dauko a kasuwar musayar 'yan wasa ta bazara:

    • Elliot Anderson: Daga Nottingham Forest zuwa Manchester City kan kuɗi kusan fam miliyan 116.
    • Mathys Detourbet: Daga Troyes zuwa Manchester City kan fam miliyan 21.4.
    • Jeremy Monga: Daga Leicester City zuwa Manchester City kan fam miliyan 10.
    • Geronimo Rulli: Daga Marseille zuwa Manchester City kan kuɗin da ba a bayyana ba.
    • Pierce Charles: Daga Sheffield Wednesday zuwa Manchester City kan kuɗin da ba a bayyana ba.
  14. Ramsay ya koma St Mirren daga Liverpool

    Dan wasan baya na gefen dama na Liverpool, Calvin Ramsay, ya koma ƙungiyar St Mirren ta Scotland a matsayin aro na tsawon kakar wasa guda.

    Dan wasan mai shekaru 23, wanda ya taba buga wa tawagar ƙasar Scotland wasa sau ɗaya, ya koma Liverpool ne daga Aberdeen a shekarar 2022 da kwantiragin shekaru biyar.

    Ramsay ya buga wasanni hudu kacal a matakin manyan 'yan wasa tare da Liverpool, amma har yanzu bai taba taka leda a gasar Premier League ba.

    Ficewarsa daga Anfield ya ba Liverpool damar samun gurbi domin daukar wani dan wasa da ba ya cikin rukunin 'homegrown' (wanda aka horar a gida).

    Dokokin gasar sun tanadi cewa kungiyoyi za su iya yi wa aƙalla 'yan wasa 17 rajista waɗanda ba sa cikin rukunin 'homegrown'.

    Ana ɗaukar dan wasa a matsayin 'homegrown' idan, ba tare da la’akari da ƙasarsa ko shekarunsa ba, ya kasance yana da alaƙa da wata ƙungiya a Ingila ko Wales na tsawon cikakkun kakanni uku ko watanni 36 kafin ya cika shekara 21 da haihuwa.

    A farkon wannan watan, zuwan Ronald Araujo Liverpool ya sa adadin 'yan wasan da ba 'homegrown' ba ya kai 17, wanda shi ne iyakar adadin da aka amince da shi.

  15. Aston Villa ta fara tattaunawa da Crystal Palace kan Mateta

    Aston Villa ta fara tuntuɓar Crystal Palace domin yiwuwar ɗaukar ɗan wasan gaba Jean-Philippe Mateta.

    Villa na nazarin zaɓuɓɓukanta wajen ƙarfafa harin ƙungiyar, musamman yayin da Al Hilal ta Saudiyya ke ƙoƙarin ɗaukar fitaccen ɗan gabanta Ollie Watkins.

    Haka kuma, Villa ta tuntubi AC Milan kan yiwuwar sayen ɗan wasan gefe Rafael Leao, kamar yadda Sky Sport Italia ta fara ruwaito wa.

    Mateta, wanda saura shekara guda kacal a kwantiraginsa da Crystal Palace, ya daɗe yana cikin jerin 'yan wasan da Villa ke sha'awarsu tun daga kasuwar musayar 'yan wasa ta lokacin hunturun da ya gabata.

    Baya ga Mateta, Aston Villa na kuma bibiyar ɗan wasan gaban Chelsea, Nicolas Jackson. Ana sa ran Jackson zai bar Chelsea kafin rufe kasuwar musayar 'yan wasa, sai dai kuma yana jan hankalin Napoli da wasu ƙungiyoyi da dama.

    Wannan na nuna cewa Aston Villa na shirye-shiryen neman sabon ɗan gaba, musamman idan Ollie Watkins ya amince da tayin komawa Al Hilal.

  16. Tottenhma ta shiga kasuwar saye da sayerwa da karfinta

    Ga jerin 'yan wasan da Tottenham ta dauko zuwa yanzu a wannan kasuwar musayar 'yan wasa:

    • Savinho (Manchester City zuwa Tottenham) – £75m
    • Sandro Tonali (Newcastle United zuwa Tottenham) – £100m
    • Mateus Fernandes (West Ham United zuwa Tottenham) – £85m
    • Jan Paul van Hecke (Brighton zuwa Tottenham) – £52m
    • Marcos Senesi (Bournemouth zuwa Tottenham) – Kyauta
    • Andrew Robertson (Liverpool zuwa Tottenham) – Kyauta
    • Martin Dubravka (Burnley zuwa Tottenham) – Kyauta

    Wannan na nuna cewa Tottenham ta kashe kuɗi masu yawa a wannan bazarar, inda ta zuba aƙalla fam miliyan 312 kan manyan saye uku da huɗu, ba tare da ƙididdige kuɗaɗen kari da sauran tanade-tanaden da ke cikin kwantiragi ba.

    Zuwa yanzu, sayen Sandro Tonali kan £100m shi ne mafi tsada, sai Mateus Fernandes (£85m) da kuma Savinho (£75m). Haka kuma, ƙungiyar ta ƙara ƙarfafa tsaro da gogewa ta hanyar ɗaukar Marcos Senesi, Andrew Robertson da Martin Dubravka ba tare da biyan kuɗin saye ba.

    Idan har Tottenham ta kammala sayen Omar Marmoush daga Manchester City, kuɗin da ta kashe a wannan bazarar zai ƙara tashi sosai, lamarin da ke nuna aniyarta ta gina ƙungiya mai ƙarfin lashe manyan kofuna a kakar wasa mai zuwa.

  17. Ina batun Marmoush da Tottenham?

    Savinho ya bayyana Roberto De Zerbi a matsayin ɗaya daga cikin "fitattun masu horarwa a duniya" bayan ɗan wasan gaba ya kammala komawarsa daga Manchester City zuwa Tottenham Hotspur.

    Da yake magana da shafin yanar gizon Tottenham bayan sanya hannu a kungiyar da ta lashe Europa League ta 2025, tauraron na Brazil ya ce:

    "An ɗauki lokaci kafin komai ya kammala amma ina matuƙar farin cikin kasancewa a nan.

    Wannan babbar dama ce a wata ƙungiya mai girma tare da ɗaya daga cikin mafi kyawun masu horarwa a duniya.

    Da zarar na yi magana da kocin, nan take na san cewa dole ne in zo. Ya gaya mini cewa yana son taimaka mini wajen kaiwa mataki mafi girma, kuma na yi imanin za mu iya cimma hakan tare, a matsayin ƙungiya."

  18. Ethiopia na neman ɗaukar nauyin AFCON 2028

    Habasha ta miƙa buƙatarta a hukumance domin karɓar baƙuncin gasar Kofin Nahiyar Afirka AFCON ta shekarar 2028, wanda zai zama karo na farko da ƙasar za ta shirya gasar cikin fiye da rabin ƙarni.

    Hukumar Kwallon Kafar Habasha ta tabbatar da gabatar da takarar a wani saƙo da ta wallafa a shafin X a daren Litinin.

    A karo na ƙarshe da Habasha ta karɓi bakuncin gasar shi ne a shekarar 1976.

    Habasha ita ce ƙasa ta biyu mafi yawan jama'a a Afirka, inda ake hasashen tana da mutane kusan miliyan 130.

    Bugu da ƙari, babban birninta Addis Ababa ne hedkwatar Tarayyar Afirka (AU). Haka kuma, Addis Ababa ne babban birnin ƙasa mafi tsayi da ke kan tudu a Afirka, tana da tsayin mita 2,300 daga matakin teku.

    Sai dai takarar na fuskantar ƙalubale da dama, ciki har da tashe-tashen hankula da har yanzu suke gudana a jihohin Amhara da Oromia, waɗanda su ne jihohi mafiya yawan jama'a a ƙasar.

    Har ila yau, akwai fargabar sake barkewar yakin basasa tsakanin gwamnatin tarayya da yankin Tigray da ke arewacin ƙasar.

    Tawagar ƙwallon ƙafar Habasha tana matsayi na 143 cikin ƙasashe 211 a jadawalin FIFA.

    Haka kuma, karo na ƙarshe da ta buga gasar AFCON shi ne a shekarar 2022, inda aka fitar da ita tun daga matakin rukuni.

  19. Man City da Tottenham na rige-rigen ɗaukar Cody Gakpo

    Manchester City ta shiga cikin jerin kungiyoyin da ke neman daukar ɗan wasan gaba na Liverpool da ƙasar Netherlands, Cody Gakpo mai shekaru 27, yayin da Tottenham Hotspur ma ke ci gaba da kokarin kulla yarjejeniya da shi.

  20. Manchester City ta amince da sayen Allan Elias daga Palmeiras

    Manchester City ta cimma yarjejeniya da Palmeiras kan ɗaukar ɗan wasan gefe na Brazil Allan Elias a wani ciniki da zai iya kaiwa har fam miliyan 34.2.

    An shirya Allan Elias mai shekaru 22 ya maye gurbin ɗan uwansa ɗan ƙasar Brazil Savinho, wanda ake sa ran zai koma Tottenham Hotspur.

    City za ta biya kuɗin farko na fam miliyan 32, sannan a ƙara wasu fam miliyan 2.2 a matsayin ƙarin kuɗaɗen da suka danganci wasu sharudda. Ana kuma sa ran ɗan wasan zai yi gwajin lafiya cikin kwanaki masu zuwa.

    A gefe guda kuma, City na ci gaba da tattaunawa kan sayar da ɗan wasan gaba na Masar Omar Marmoush zuwa Tottenham.

    Majiyoyin da ke da masaniya kan lamarin sun ce akwai "kyakkyawar dama" yarjejeniyar za ta kammala kafin rufe kasuwar musayar 'yan wasa ranar 1 ga Satumba.

    Har yanzu dai tattaunawa na ci gaba tsakanin kulob ɗin biyu, duk da cewa akwai wasu bayanai da sharudda da ba a kammala daidaitawa a kansu ba.

    Haka kuma, ɗan wasan tsakiya Nico Gonzalez na iya barin filin wasa na Etihad kafin rufe kasuwar musayar 'yan wasa, inda Newcastle United ke nuna sha'awa wajen ɗaukar ɗan wasan na Spain.