Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 20 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Ahmad Bawage

  1. Abin da muka sani kan 'sace mutum 160' a Kaduna

    Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce babu gaskiya a rahotannin da ake yaɗawa na garkuwa da sama da mutane 160 a wasu coci-coci da ke ƙauyen Kurmin Wali a ƙaramar hukumar Kajuru ta jihar Kaduna.

    Rundunar ta ce wasu marasa kishi ne ke yaɗa wannan labari da nufin tayar da hankalin jama'a.

    A ranar Litinin jaridun Najeriya da dama sun bayar da rahoton sace mutane fiye da 100 a wuraren ibadah daban-daban na ƙauyen Kurmin Wali, inda suka ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi 18 ga watan Janairu.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa shugaban ƙungiyar kiristoci ta Najeriya CAN, reshen jihar Kaduna Reberan Joseph John Hayab ya tabbatar mata da aukuwar lamarin, in da ya ce: "duk da cewa ban cika son ambata adadi ba, amma bayanan da na samu daga yankin na nuna cewa ƴanbindiga sun sace kusan mutum 172, amma guda 9 sun tsere sun koma gida, amma har yanzu ana neman mutum 163,"

    Amma rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce har yanzu babu wasu bayanai da suka tabbatar da cewar an ɗauke mutanen.

  2. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Talata

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.