Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na 20 ga watan Maris 2025

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Nabeela Mukhtar Uba da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Iran ta sako wani ɗan Faransa da take riƙe da shi tun 2022

    Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce Iran ta sako wani ɗan ƙasar da ake tsare da shi tun watan Oktoban 2022.

    An tsare Olivier Grondeau ne bisa dalilai na tsaro bayan kama shi da akayi a birnin Shiraz da ke kudancin ƙasar.

    Shugaba Macron ya tabbatar da dawowar Mista Grondeau zuwa Faransa sai dai babu wasu cikakkun bayanai kan sharuɗɗan sako shi.

    Mista Macron ya kuma buƙaci a sako sauran ƴan ƙasarsa biyu da ake riƙe da su a gidajen yari da ke Iran.

    Ƙasashen yamma dai sun daɗe suna zargin Iran da tsare ƴan ƙasashen waje ba tare da dalili ba domin yin amfani dasu a matsayin wani abin yin yarjejeniyar diflomasiyya.

  2. Finland ce ƙasar da al'ummarta suka fi farin ciki a duniya karo na takwas a jere

    An sanya Finland a matsayin ƙasa da alummarta suka fi farin ciki a duniya shekara takwas a jere.

    Masana sun yi amannar cewa yankin da ƙasar Finland take, da damar da ƴan ƙasar suke da ita na samun tsarin walwala mai inganci, sun taimaka wajen ganin ƙasar ta ci gaba da kasancewa ta ɗaya a rahoton ƙasashe da al'umominsu suka fi farin ciki ta Majalisar ɗinkin duniya.

    Rahoton ya bayyana ƙasar Denmark a matsayin ƙasa ta biyu da al'ummarta suka fi farin ciki a duniya.

    A karon farko Costa Rica da Mexico sun shiga jerin ƙasashe 10 da al'umominsu suka fi farin ciki inda rahoton ya yi misali da yadda iyalai ke zumunci a waɗannan ƙasashe.

    Sai dai Amurka da Koriya ta Kudu sun yi ƙasa a teburin, sakamakon karuwar da ake samu na yawan masu kashe kansu da masu shan miyagun kwayoyi.

  3. Hare-haren Isra'ila cikin dare sun hallaka mutum aƙalla 50 a Gaza

    Ƙungiyar bada agaji ta Civil defence a zirin Gaza ta ce hare-hare ta sama da Isra'ila ta kai cikin dare sun yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 50 ciki harda yara ƙanana.

    Hamas wadda zirin Gaza ke ƙarƙashin ikonta ta ce ta yi alla wadai da farmaki ta kasa na sojoji Isra'ila kuma ta bayyana shi a matsayin abinda ya saɓawa yajejeniyar tsagaita wuta na watanni biyu.

    Rahotanni sun ce hare-haren da Isra'ila ta kai tun ranar Litinin wanda ya kawo ƙarshen yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta da Hamas, sun shafi wata makaranta da ake tsugunar da waɗanda suka rasa muhalansu.

    Tun da farko Ministan tsaron Isra'ila, Isreal Katz ya gargaɗi almummar Gaza akan cewa za a lalata yankin bakiɗaya idan ba su dawo da waɗanda aka yi garkuwa da su ba tare da katse duk alaƙa da Hamas.

  4. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafinmu na kai tsaye na sashen Hausa na BBC, barkanmu da safiyar Alhamis, a yau ma za mu kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa Najeriya da ma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo da kuma yin muhawara.

    Ku kasance tare da mu.