Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na 11 ga watan Fabrairun 2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi, Ahmad Bawage da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Kwamitin gudanarwa na Jam'iyyar PDP ya tabbatar da Udeh-Okoye a matsayin sakataren jamiyyar na kasa

    .

    Asalin hoton, PDP

    Kwamitin gudanar wa na Jam'iyyar PDP ya tabbatar da Sunday Ude-Okoye a msatyin sakataren jam'iyyar na kasa.

    Jarridar The Punch ta ce hakan dai na cikin wata sanarwa da kwamitin gudanarwar ya fitar mai dauke da sa hannun sakatren yada labarai na jam'iyyar ta PDP na kasa Debo Ologunagba ya fitar a yau Laraba.

    Sanarwar ta ce ta dauki wanna mataki ne domin yin biyayya ga hukuncin da kotun daukaka kara ta yi kan batun.

    Haka kuma sanarwar ta ambato, cewar tuni ta aikawa da Hukumar zaben Najeriya mai zaman kanta INEC, matsayar da suka cimma na tabbatar da Sunday Udeh-Okoye a matsayin halattacen sakataren jam'iyyar tasu na kasa, da sauran dukkan hukumomin da suka kamata, kamar yadda hukucin kotun daukaka karar ya bayar da hukunci.

    "Kwamitin gudanarwa na jam'iyyar PDp a zaman da muka yi a yau Laraba, 12 ga watan Fabarerun, 202, mun amince da wannan takarda mai kwanan watan 11 ga watan Fabarerun, 2025, ga shugaban jam'iyyar mu na ruko, kan dukkan wani batu da ya shafi dambarwar sakatren jam''iyyar PDP.

  2. sakataren MDD

    Asalin hoton, AP

    Babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya ce wajibi ne a kaucewa ci gaba da yaƙi a Gaza wanda hakan zai iya kaiwa ga tashin hankali mai muni.

    A shafinsa na X, ya ce yana buƙatar Hamas ta ci gaba da shiin da aka amince da shi na sakin mutanen da aka yi garkuwa da su.

    Ya kuma gargaɗi ɓangarorin biyu cewa dole su bi ka'idojin yarjejeniyar tsagaita wutar kuma su ci gaba da tattaunawa.

    Wannan dai na zuwa ne a daida lokacin da alamu ke nuna yarjejeniyar ka iya wargajewa bisa musayar yawu da ake tsakanin ɓangarorin biyu.

  3. Fitar da Falasɗinawa daga ƙasarsu babban laifi ne - al-Sharaa

    al-Sharaa

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Syria, Ahmed al-Sharaa ya ce Donald Trump ya samu dama ta "fara zangonsa na biyu", a wata hira da ya yi.

    Ya yi kira ga shugaban na Amurka da ya yi watsi da dukkannin takunkuman da Amurkar ta ƙaƙaba wa Syria inda ya ce yanzu gwamnatin ta sauya.

    To sai harshensa ya sauya lokacin da aka tambaye shi ra'ayinsa dangane da batun kwashe Falasɗinawa daga Gaza, sai ya ce "babu wani dalili na hankali ko shari'a da ta bai wa Trump damar jagorantar sauya wa Falasɗinawa matsuguni zuwa wurin da ba ƙasarsu ba." In ji al-Sharaa.

    Ya kuma ƙara da bayyana yunƙurin da "babban laifi wanda ba zai samu nasara ba daga ƙarshe,"

  4. Mun bai wa Hamas wa'adin Asabar ta saki mutanenmu - Netanyahu

    Netanyahu

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya ce ya bai wa Hamas wa'adi zuwa ranar Asabar da su saki mutanen da suke garkuwa da su kamar yadda aka amince a yarjejeniyar tsagaita wuta ko kuma yarjejeniyar ta wargaje.

    Netanayhu ya ce ya yi ganawa ta awa huɗu da majalisar yaƙinsa inda kowa ya bayyana kaɗuwa da halin da mutane uku da Hamas ta saka ranar Asabar suka kasance.

    "Dukkanin mu mun yi maraba da buƙatar shugaba Trump na sakin mutanen zuwa ranar Asabar da rana, sannan za mu yi maraba da shirin da shugaban yake da shi na makomar Gaza."

    "Bisa la'akari da sanarwar da Hamas ta fitar na karya yarjejeniyar tare da ƙin sakin waɗanda ake garkuwa da su, a jiya da daddare, na umarci IDF da su haɗa kan sojoji a ciki da kewayen Gaza. Wannan aikin zai faru ne a sa'annin nan. Za a kammala nan ba da jimawa ba.

    "Shawarar da muka yanke a majalisar ministoci ita ce: Idan har Hamas ba ta dawo mana da waɗanda take garkuwa da su ba da ranar Asabar - za a kawo ƙarshen yarjejeniyar kuma dakarun IDF za su koma yaƙar Hamas har zuwa lokacin da za a samu galaba a kansu." In ji Netanyahu.

  5. Isra'ila ce ke karya alƙawuran yarjejeniyar tsagaita wuta - Erdogan

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan ya ce Isra'ila ta "gaza cika alƙawurran da ta ɗauka" dangane da yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza.

    Erdogan ya ƙara da cewa " dole ne mamayar Isra'ila ta zo ƙarshe". Mamayar da suke ce ƙashin bayan duk wata matsala."

    Mista Erdogan ya ce zai aike da talalfin kayan agaji zuwa Gaza kuma zai ci gaba da yin hakan, inda ya yi kira da aka kafa ƙasar Falasɗinawa mai cin gashin kanta.

  6. Ƙungiyar Houthi ta gargaɗi Isra'ila kan sake yaƙar Falasɗinawa

    Houthis

    Asalin hoton, AP

    Ƙungiyar Houthi mai samun goyon bayan ƙasar Iran ta gargaɗi Isra'ila cewa a shirye take ta afka wa Isra'ilar idan har ta koma kai hare-hare a Gaza.

    Shugaban ƙungiyar ta Houthi, Abdul Malik al-Houthi ne ya yi kalaman na gargaɗi ne a wani jawabi da ya yi a gidan talbijin kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.

    Tundai bayan da yaƙin Gaza ya fara, ƙungiyar ta Houthi da ke Yemen sun ƙaddamar da hare-haren jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami duk da cewa Isra'ila ta yi iƙrarin kama wasu.

    Ƴan ƙungiyar ta Houthi sun kai hare-hare kan jiragen ruwa a tekun maliya da mashigar Aden da suka ce suna yi ne domin nuna goyon baya ga al'ummar Falasɗinawa.

  7. Ba na jin tsoron a kama ni - El-Rufa'i

    El Rufai

    Asalin hoton, OTHERS

    Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El- Rufai ya ce ba zai yi gudun hijira ba duk da raɗe-raɗin da ake yi na cewa ana shirin kama shi tare da azabtar da shi.

    El Rufai ya faɗi haka ne a martanin da ya mayar a shafinsa na X bayan wani mai amfani da shafin ya wallafa cewa ya samu bayanai masu ƙarfi da ke nuna ana shirin kama El Rufai.

    ''Na daɗe ina jin waɗannan raɗe-raɗin kan kama ni da tsare ni da kuma azabtar da ni a wani ɗakin azabtarwa da ke ofisihin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro ( wurin da ake zargin an azabtar ta Emefiele domin ya bar aiki a matsayin gwamnan CBN), tun watan Yulin 2024 lokacin da aka fara yaɗa rahoton majalisar dokokin jihar Kaduna'' in ji shi.

    Ya kuma ce an aika irin waɗannan sakonnin barazanar ta hanyar abokai da ƴan uwanshi da dama saboda ana so ya yi ji tsoro ya yi gudun hijra da kanshi, sai da El Rufai ya ce '' ba zan yi hakan ba''.

    Ya ce kafin ranar 20 ga watan Fabrairu zai dawo Najeriya, ya kuma ce ya dakatar da karatun da yake yi da kuma shirin koyon wasu harsuna zai dawo gida Najeriya, domin a cewarsa ba zai ci gaba da yin shiru ba.

    El Rufai ya kuma ce kamawa da tsarewa da kuma azabtar da abokan hamayya a siyasa ba sabon abu ba ne, ''ni kaina an kama ni kuma an kulle ne sau uku a baya saboda bayyana ra'ayi na kan gwamnatocin baya.'' a cewarsa.

    A ƴan kwanakinnan dai ana ta samun ce-ce-ku-ce tsakanin tsohon gwamnan Kaduna El Rufai da ƴaƴan jam'iyya mai mulki na APC da kuma rashin jituwa da ake zargin akwai tsakaninsa da gwamnan jihar na yanzu Uba Sani.

  8. Jigawa za ta ƙulla hulɗa da Saudiyya don bunƙasa noman dabino

    ...

    Asalin hoton, Namadi/ Facebook

    Gwamnatin jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya za ta ƙulla hulɗar kasuwanci tsakaninta da wani kamfanin Saudiyya da ke noman dabino domin bunƙasa noman dabino a jihar.

    Gwamnan jihar Umar Namadi ne ya bayyana haka a lokacin da ya karɓi baƙuncin ma'aikatan kamfani mafi girma a Saudiyya a fannin noman dabino da kula da aikin gona, karƙashin jagorancin Abdul'aziz Abdurrahman Al-Awf a Dutse, babban birnin jihar.

    Abdul'aziz Al-Awf ya ce kamfaninsu za ta samar da tsarin noma na zamani domin ganin an yi noman dabino a tsawon shekara ba sai kaka ba, wanda za a cimma ta hanyar horar da manoma, karfafawa matasa da kuma amfani da wasu daga cikin ire-iren dabino na Saudiyya da ke samar da amfani mai yawa ta yadda jihar za ta zama kan gaba a noman dabino a Najeriya da Afrika.

    Gwamnan jihar ya bayyana cikkakiyar goyon bayansa ga shirin, inda ya ce hakan ya yi dai-dai da manufarsa ta bunƙasa fannin noma.

    Ya ce ko a yanzu ma jihar ce ta fi kowacce samar da dabino a Najeriya, kuma burinsu shi ne samar da adadin dabinon da ake buƙata a ƙasar har ma a fitar da shi ƙasashen waje.

    Samfurin dabino na Mejdool (Meju) da Barhi (Bari) da Sukkari (Sukari) da kuma Ajwa ne aka bayyana a matsayin waɗanda suka dace a yi noman su a Jigawa.

  9. Wata malama ta daɓa wa ɗaliba wuƙa har lahira a Koriya ta Kudu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana zargin wata malamar makaranta da kashe wata ɗaliba ƴar shekara takwas sakamakon daɓa mata wuka a makarantar Firamare da ke tsakiyar birnin Daejeon da ke kudancin Seoul a Koriya Ta Kudu.

    Ƴansanda sun ce malamar ta kuma ji wa kanta ciwo da wukar da gangan.

    Malamar ta amsa laifin cewa ita ta daɓa ma yarinyar wuƙa, sai dai babu wani bayani kan dalilin yin hakan.

    Ƴansandan ƙasar sun ce malamar ta koma aiki kwanaki 20 bayan ta nemi hutun wata shida saboda matsalar kwakwalwa na ciwon damuwa, inda ta zo da takardar asibiti ɗauke da bayanan likita cewa ta samu lafiyar iya komawa aiki.

  10. Ana ci gaba da gwabza faɗa a Kongo

    ƴan tawayen M23

    Asalin hoton, AFP

    Ana cigaba da gwabza yaƙi a gabashin Congo bayan tsagaitawa na kwanaki biyu.

    A safiyar yau Talata ne ƴan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda su ka kai wa sojojin ƙasar hari kusa da Ihusi, wani matsuguni da ke kusa da tafkin Kivu, da ke da nisan kilomita 70 daga arewacin birnin Bukavu.

    Mazauna garin sun ce sun ji ƙarar harbin makamai.

    Da alamu ƴan tawayen M23 sun samu karin ƙwarin gwiwa bayan ƙwace birnin Goma cikin sauƙi makonni biyu da suka gabata wanda ke nuna tsagaita wutan da aka bayyana ba lallai ya yi tasiri ba.

    A yanzu haka sun doshi kudancin tafkin.

    Taron gaggawa da akayi na yankin a ranar asabar ya buƙaci ƴan tawayen da Rwanda mai mara musu baya su kawo karshen yaƙin.

    Sai dai har yanzu Rwanda na cigaba da musanta zargin goyon bayan M23.

  11. Sufeta-Janar ya ja kunnen ƴansandan Najeriya

    Sufeta-janar na ƴansandan Najeriya

    Asalin hoton, NIGERIA POLICE/X

    Sufeto Janar na ƴan sandan Najeriya Kayode Egbetokun ya ja kunnen jami'an ƴansanda kan take hakki da ma aikata wasu laifukan.

    Egbetokun a lokacin wani taro ta intanet ya ce an kawo mishi ƙorafe ƙorafe kan take hakki da dama ta kafofin da rundunar ke karbar korafi, inda ya yi gargaɗin cewa ba za su lamunci take haƙƙin bil'adama ba kuma wanda aka kama zai fusknaci hukunci mai tsauri.

    Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Muyiwa Adejobi ya fitar, Egbetokun ya kuma gargaɗi jami'ai na musamman kan wuce gona da iri da kuma yin shigar da ba ta dace ba, inda ya jaddada muhimmancin sanya kayan da suka dace a lokacin aiki tare da haramta wa duk wanda ke sanye da kayan gida ɗaukar makami.

    Sufeton ƴansanda ya kuma buƙaci jam'ian tsaron a kowane matsayi su yi aiki tare domin kauce wa duk wani abu da zai ɓata musu suna.

  12. Harin kunar baƙin wake ya hallaka mutum biyar a Afghanistan

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Aƙalla mutane biyar sun mutu, wasu da dama kuma sun jikkata a wani harin kunar baƙin wake da aka kai a wani banki da ke arewa maso gabashin Afghanistan.

    Shaidun gani da ido sun shaida wa BBC cewa maharin ya ta da bam ɗin ne a lokacin da ƴan Taliban ke karɓar albashinsu a cikin ginin da ke yankin Kunduz.

    Zuwa yanzu babu wanda ya ɗau alhakin kai harin, sai dai mayakan IS na cigaba da ta da ƙayar baya kan ƴan Taliban tun bayan dawowa kan mulki a 2021.

  13. 'Za mu cigaba da ɗaukar matakai ba ƙaƙƙautawa har sai kowa ya koma gida'

    Firaministan Isra'ila Netanyahu

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya mika ta'aziyyarsa ga ƴan uwan Shlomo Mansour, wanda Hamas ta kashe a ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

    Netanyahu ya bayyana mamacin a matsayin wanda ya taimaka wajen gina ƙasar.

    Ya kuma ce ba za su yi shiru ba kuma ba za su huta ba har sai an mayar da gawarsa gida.

    Firaiministan ya ƙara da cewa za su cigaba da ɗaukar matakai ba ƙaƙƙautawa har sai an mayar da waɗanda aka yi garkuwa da su gida, na raye da waɗanda su ka mutu.

  14. Najeriya ce ta 140 cikin jerin ƙasashen da aka fi tafka rashawa a duniya

    Bola Tinubu

    Asalin hoton, Bola Tinubu

    Najeriya ta zama ƙasa ta 140 a cikin jerin ƙasashen da aka fi tafka cin hanci da rashawa a duniya a shekarar 2024, in ji ƙungiyar Transparency International.

    A cikin rahoton wanda ta fitar a yau, Transparency ta ce Denmark ce ƙasar da ta kasance wadda ba ta fuskantar matsalar ta cin hanci da rashawa.

    Rahoton wanda ya yi nazari kan ƙasashe 180 na duniya ya yi amfani da masana da ƴan kasuwa wajen tantance matsayin kowace ƙasa.

    Ma'auni tantance munin cin hancin ya kama ne daga maki sifili zuwa 100, inda sifili ke nufin mummunan matsalar cin hanci yayin da 100 ke nufin rashin matsalar baki ɗaya.

    Rahoton ya yi la'akari ne da ƙarfin hukumomi a ƙasashen, da inganci zaɓe da kuma ɗabi'ar gwamnati.

    Transparency International ta ce Najeriya tare da wasu ƙasashe kamar Uganda, Mexico, Madagascar, Iraq da Kamaru sun samu maki 26 ne cikin 100.

    Sudan ta Kudu da Somaliya da kuma Venezuela na cikin ƙasashen da aka fi tafka rashawa a duniya.

    Transparency ta ce cin hanci babban barazana ce ga sauyin yanayi. Ta ce hakan yana kawo cikas wajen batun rage fitar da gurɓataccen iska da masana'antu ke yi.

  15. Ɗaya daga cikin Isra'ilawan da Hamas ta yi garkuwa da su ya mutu

    Shlomo Mansour

    Asalin hoton, Hostages and Missing Families Forum

    Dakarun Isra'ila, IDF, sun ce ɗaya daga cikin Isra'ilawan da ake riƙe da su a Gaza ya mutu.

    Sun ce an kashe Shlomo Mansour ɗan shekaru 86 ne tun ranar 7 ga watan Oktoba 2023, ranar da akayi garkuwa da shi.

    Shlomo Mansour na daga cikin mutane 33 da gwamnatin Isra'ila ta fitar wanda ya kamata a sako a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta.

    Sun kuma ce sun sanar da iyalinsa mutuwar, kuma a na cigaba da rike gawarsa a Gaza.

  16. Mutanen Isra'ila nawa ne a hannun Hamas har yanzu?

    Zuwa yanzu Isra'ilawa 16 da akayi garkuwa da su aka saki

    Asalin hoton, EPA

    Hamas ta yi garkuwa da mutane 251 ta kuma kashe aƙalla 1,200 lokacin da ta kai hari Isra'ila a ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

    Hamas na kuma cigaba da rike mutane 73 da tayi garkuwa da su, da wasu uku da aka ɗauka sama da shekaru goma - wanda ake ganin ɗaya daga cikinsu ya mutu - a Gaza.

    Tun da yarjejeniyar ta soma a ranar 19 ga watan Janairun, an saki Israilawa 16 da ƴan Thailand 5 domin musayarsu da fursunoni 566.

    A ƙarshen matakin farko na yarjejeniyar nan da makonni uku, ana sa ran an saki waɗanda akayi garkuwa da su 33 da kuma fursunoni 1,900, sai dai Isra'ila ta ce 8 cikin 33 sun mutu.

    Sauran waɗanda akayi garkuwa da su za a sake su a mataki na biyu wanda har yanzu ba a kammala tattaunawa kanshi ba.

  17. Kalaman Trump za su iya lalata yarjejeniyar tsagaita wuta - Hamas

    Sami Abu Zuhri

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Sami Abu Zuhri

    Shugabannin ƙungiyar Hamas sun ce tsoma bakin da Turmp ke yi a baya-bayan nan game da Gaza na ƙara dagula batun yarjejeniyar tsagaitar da ke rawa da aka cimma tsakanin ɓangarorin biyu.

    A jiya Litinin Trump ya yi barazanar watsi da yarjejeniyar matuƙar Hamas ta gaza sakin ɗaukacin ƴan Isra'ila da take garkuwa da su.

    Ɗaya daga cikin masu magana da yawun Hamas, Sami Abu Zuhri ya ce hanya ɗaya tilo ta tabbatar da cewa dukkanin waɗanda ake garkuwa da su sun koma gida ita ce ta hanyar martaba yarjejeniyar da aka cimma a watan jiya sau-da-ƙafa.

    A jiya Litinin, Hamas ta yi barazanar jinkirta sakin sauran ƴan Isra'ila da take riƙe da su bisa zargin Isra'ilar da rashin martaba ƙa'idojin yarjejeniyar yadda ya kamata.

    Hujjojin da Hamas ta bayar sun haɗa da cewa Isra'ila na yin cikas ga shigar kayan agaji zuwa Gaza da kuma sakin Falasɗinawan da ke hannunta.

    Isra'ila ta yi watsi da zargin, sannan tana ƙara yawan dakarunta a kusa da yankin.

  18. Jirage ɗauke da ƴan Venezuela daga Amurka sun isa gida

    Shugaban Venezuela Nicolas Maduro

    Asalin hoton, Getty Images

    Jirage biyu ɗauke da ƴan Venezuela kusan 200 da aka kwashe daga Amurka sun isa birnin Caracas na kasar Venezuela.

    Su ne kashi na farko da aka kwashe ƙarƙashin yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin gwamnatin Trump da shugaba Nicolas Maduro.

    Dangantakar diplomasiyya ta yi tsami tsakanin Amurka da Venezuela tsawon shekaru masu yawa.

    Sai dai Mista Maduro na ƙoƙarin daidaita al'ammura da fatan cewa Amurkar za ta janye wasu daga cikin takunkuman tattalin arziƙi da ta sanya wa ƙasar.

  19. Za mu soke yarjejeniyar tsagaita wuta idan Hamas ba ta saki sauran Isra'ilawa ba

    Shugaban Amurka Trump

    Asalin hoton, Others

    Shugaba Trump ya ce idan har Hamas ba ta saki sauran Isra'ilawan da take garkuwa da su a Gaza ba zuwa tsakar ranar Asabar, Isra'ila za ta soke yarjejeniyar tsagaita wuta, sannan ayi duk bala'in da za'ayi.

    Ya kuma ce zai iya dakatar da tallafin da suke ba ƙasashen Jordan da Masar idan har suka ƙi amincewa ya tsugunnar da Falasdinawa da yake son kwashewa daga Gaza.

    Kalaman na sa na zuwa ne bayan sanarwar da Hamas ta yi na dakatar da sakin Isra'ilawan da ta yi garkuwa da su har sai abunda hali ya yi, inda ta zargi Isra'ila da karya dokokin tsagaita wuta.

  20. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barkan mu da safiyar Talata.

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa.

    Ku kasance da mu domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwaɓtanta da kuma sauran sassan duniya.

    Da fatan za ku kasance da mu a shafuakan sada zumunta: Facebook, X, Instagram, YouTube da WhatsApp domin tafka muhawara kan labaran da muke kawo muku.