Haɗarin jirgin ƙasa a Portugal ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 15
Aƙalla mutane goma sha biyar ne suka mutu, yayin da 18 su ka jikkata bayan da wani jirgin ƙasan fasinja ya kauce hanya ya kuma yi haɗari a Lisbon babban birnin kasar Portugal.
Jirgin mai ɗaukar fasinjoji kusan arba'in ya lalace sakamakon yin karo da wani gida bayan ya sauka daga layin dogo.
Wata mata da ta shaida faruwar lamarin ta ce jirgin ya faɗi ne kusa da inda su ke wanda ya sa su barin wurin a guje.
Har yanzu dai ba a san musabbabin faruwar lamarin ba, sai dai tuni aka kaddamar da bincike.
Magajin garin birnin na Lisbon ya bayyana lamarin a matsayin 'Mummunar rana' ga birnin da kuma gwamnatin Portugal.