Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 10/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 10 ga watan Agustan 2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Trump ya bukaci Iran ta biya diyyar sojojin Amurka da fararen hular da ta kashe

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya bukaci Iran ta biya diyyar sojojin Amurka da fararen hular da ya ce Iran ta kashe ko raunata su a hare-hare daban-daban da ta kai.

    Trump ya bayyana hakan ne bayan wasu jami'an Iran sun bukaci Amurka ta biya diyya kan ɓarnar da suka ce ta yi wa Iran a cikin watanni biyar na rikicin da kasashen biyu suka yi.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce batun biyan diyya bai taba tasowa ba a tattaunawar da Amurka da Iran suka yi.

    Ya ce: "Amma wannan ra'ayi ne mai ban kyau, domin yanzu ina bukatar Iran ta biya diyya kan duk mutanen da ta kashe ko ta jikkata."

    Trump ya kuma zargi Iran da hannu wajen kashe ko raunata sojojin Amurka ta hanyar bama-bamai da aka dasa a gefen tituna da kuma wasu hare-hare da ya ce an kai a karkashin jagorancin Janar Qassem Soleimani.

    Trump ya ce ya umurci wakilan Amurka da su gabatar da buƙatar diyya tare da neman a cimma matsaya a kansa a duk wata tattaunawa da za a yi nan gaba da Iran.

    Ya kuma bukaci Iran ta biya diyya ga iyalan daruruwan dubban masu zanga-zangar da ya zargi gwamnatin Iran da kashewa cikin shekaru 50 da suka gabata.

    A cewar Trump, ya kamata a kuma biya diyya kan mutanen da ya ce an kashe a cikin watanni biyar da suka gabata.

  2. Gwamnatin Kano ta ƙara wa malaman jami'a albashi

    Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da ƙarin albashi ga malamai da sauran ma'aikatan jami'o'in jihar.

    Ƙarin zai shafi jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil da Jami'ar Northwest.

    Gwamnan ya amince da ƙarin ne bayan wani kwamiti da majalisar zartarwar jihar ta kafa ya duba buƙatar jami'o'in biyu na mayar da sabon tsarin albashin cikin tsarin jihar.

    Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Litinin ta ce sabon tsarin ya fara aiki daga watan Janairun 2026, inda za a fara biyan ƙarin kuɗin daga watan Satumban 2026.

    Ƙarin albashi a jami'o'in biyu a yanzu zai laƙume kusan naira miliyan 391.8 duk wata, wanda ya kai sama da naira biliyan 4.7 a shekara.

    Ta ƙara da cewa hakan ya biyo bayan sabon tsarin albashin da gwamnatin tarayya ta fara amfani da shi a jami'o'in tarayya.

  3. Al'ummar Kano ba su tare da kalaman Sheikh Jingir - Kwankwaso

    Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce kalaman da malamin addinin musulunci Sheikh Sani Yahaya Jingir ya yi na iya haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin al'ummar Najeriya.

    A wata sanarwa da Kwankwaso ya wallafa a shafinsa na X, ya jaddada cewa al'ummar Kano ba su tare da irin waɗannan kalamai na yunƙurin rarraba kawuna ba

    Ya ce ya damu matuƙa da kalaman da Sheikh Jingir ya yi a wani taro a Kano a ƙarshen mako.

    A ƙarshen makon nan ne kafar sada zumunta da ma kafafen yada labarai suka ɗauki ɗimi da musayar yawu da cece-kuce kan kalaman da shugaban majalisar malamai ta ƙungiyar Izala, Sheikh Sani Yahaya Jingir ya yi dangane da takarar Muslim-Muslim.

    Kwankwaso wanda mataimakin ɗantakarar shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC Peter Obi ne, ya ce abin damuwa ne ganin irin waɗannan kalamai suna fitowa daga bakin malamin addinin da ke da matsayi da tasiri a tsakanin al'umma.

    “Bai kamata mu yi amfani da muryarmu wajen faɗin kalaman da za su iya raunana haɗin kan ƙasarmu ba.”

    Ya ce a wannan lokaci da Najeriya ke ciki, ya kamata a yi watsi da duk wasu kalaman da ka iya haifar da rashin haɗin kai.

  4. An gano kaburbura masu tarin gawawwaki a kudu maso gabashin Sudan

    An gano kaburbura da ke ɗauke da gawarwakin fararen hula 25 a garin Kurmuk na jihar Blue Nile da ke kudu maso gabashin Sudan.

    Jami'an yankin sun zargi dakarun RSF da kashe mutanen kafin nan suka binne su a kaburburan.

    Kwamishinan Kurmuk, Abdel Aty Mohamed al-Faki, ya ce an gano kaburburan ne bayan sojojin Sudan sun sake ƙwace garin daga hannun RSF a watan Yuli.

    Ya ƙara da cewa an kashe mutanen ne a kusa da tsaunin Jebel Fankat, inda RSF ke amfani da shi wajen kai hare-haren jiragen sama marasa matuƙa.

    Kungiyoyin kare haƙƙin bil'adama sun daɗe suna zargin RSF da aikata kisan gilla da tilasta wa mutane yin gudun hijira a yankin Blue Nile.

  5. Mayaƙan ISWAP sun kai wa sojojin Najeriya hari da manya-manyan gurneti

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun daƙile wani mummunan hari da mayaƙan ƙungiyar ISWAP suka kitsa kan wani sansanin soji da ke jihar Borno, arewa maso gabashin ƙasar.

    Hakan na zuwa ne yayin da mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da kai hare-hare akai-akai kan jami'an tsaro da kuma al'umma fararen hula a yankin.

    Mayaƙan na ISWAP sun yi yunƙurin kai harin ne da tsakar daren ranar Lahadi kan sansanin sojin Najeriya da ke Gajiram a ƙaramar hukumar Nganzai da ke jihar ta Borno.

    A cikin wata sanarwa da dakarun Operation Hadin Kai suka fitar, ta ce: "sojoji sun daƙile harin ta hanyar mayar da martani da ƙarfin gaske, lamarin da ya tursasa wa maharan janyewa bayan sun tafka hasara. Sojojin sun kuma samu nasarar ƙwato makamai da alburusai da kuma na'urorin sadarwa daga maharan.

    "Bidiyon da aka ɗauka ya nuna yadda maharan suka kwashe ƴan'uwansu da aka kashe da kuma waɗanda suka samu rauni daga wurin," a cewar sanarwar.

    Sai dai sojojin sun bayyana cewa an yi musu ɓarna kasancewar maharan sun yi amfani da manya-manyan gurneti wajen kai wa sansanin hari, wanda hakan ya yi sanadiyyar lalata motocin soji da wasu kayan aiki.

    Sai dai sojojin ba su bayyana ko akwai sojan da ya rasa ransa ba.

  6. Kashim zai kwashe mako biyu yana karatu da nazari kan rayuwa

    Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, zai kwashe mako biyu yana karatu da yin nazari kan rayuwa da harkokin shugabanci yayin hutunsa na makwanni biyu, a cewar mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha.

    Ya ce hutun zai ba Shettima damar zurfafa ilimi da kuma yin tunani kan muhimman batutuwan da suka shafi aikinsa da hidimarsa ga Najeriya.

    Stanley Nkwocha ya bayyana cewa Shettima ya saba amfani da irin wannan lokaci wajen nazari da koyo, yana mai jaddada cewa shugabanci mai ɗorewa na buƙatar mutum ya ci gaba da neman ilimi a kowane lokaci.

    Ya ce nisantar ayyukan yau da kullum na ɗan lokaci na ba wa shugaba damar sake duba ra’ayoyi da tsare-tsare cikin natsuwa domin komawa aiki da sabbin tunani.

    Mai magana da yawun mataimakin shugaban ƙasar ya ƙara da cewa koyon sabbin abubuwa ba ya tsaya wa idan mutum ya samu babban matsayi, sai dai ma ƙarin nauyin aiki yana ƙara nuna muhimmancin ci gaba da neman ilimi.

    Ya ce wannan lokaci na karatu da nazari zai taimaka wa Shettima wajen ƙara fahimta da ƙwarewar da ake buƙata domin ci gaba da yi wa Najeriya hidima.

  7. Sojojin 10 sun mutu yayin da suka kashe masu iƙirarin jihadi 40 - Mali

    Hukumomin ƙasar Mali sun ce sojojinsu sun kashe kimanin mayaƙan jihadi 40 bayan da aka kai hari wani sansanin soji a yankin San na jihar Ségou da ke tsakiyar ƙasar.

    Sai dai kamfanin dillancin labaran AFP ya ruwaito cewa aƙalla sojoji 10 ne suka mutu a harin, kuma maharan sun ɗan ƙwace sansanin na ɗan lokaci kafin sojojin gwamnati suka sake karɓe shi.

    Rundunar sojin Mali ta ce ta daƙile harin cikin nasara, yayin da ƙungiyar JNIM mai alaƙa da al-Qaeda ta yi iƙirarin cewa ta mamaye sansanin.

    Harin na zuwa ne yayin da matsalar tsaro ke ƙara taɓarɓarewa a Mali, inda ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi ke ƙara kai hare-hare a sassa daban-daban na ƙasar.

  8. Diflomasiyya kaɗai ba za ta kawo ƙarshen rikicin mashigar Hormuz ba - Iran

    Iran ta ce ba za a iya kawo ƙarshen rikicin da ke tattare da mashigar Hormuz ta hanyar diflomasiyya kaɗai ba, tana mai jaddada cewa dole ne a haɗa tattaunawa da amfani da ƙarfin ƙasa wajen kare muradunta.

    Mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana cewa diflomasiyya na taka muhimmiyar rawa wajen kare bukatun ƙasar, amma ba za ta wadatar ba muddin akwai abin da ya kira matsin lamba da takunkumin ruwa da Amurka ke amfani da shi.

    A cewarsa, Iran na haɗa hanyoyin diflomasiyya da ƙarfin soja domin tunkarar ƙalubalen da take fuskanta, yana mai cewa wannan ne matakin da ƙasar ke ɗauka a halin yanzu.

    Ya kuma ce duk da ci gaban tattaunawar Iran da Oman kan tsara hanyar zirga-zirga a mashigar Hormuz, hakan ba yana nufin za a sake buɗe mashigin gaba ɗaya ga zirga-zirgar jiragen ruwa ba.

  9. Shugaban WHO ya buƙaci shugabannin Habasha su zaɓi tattaunawa maimakon yaƙi

    Babban Daraktan Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), Tedros Adhanom, ya buƙaci shugabannin gwamnatin Habasha da na yankunan su nemi mafita ta hanyar tattaunawa maimakon amfani da ƙarfin soja wajen warware rikice-rikicen ƙasar.

    Ya ce ci gaba da yaƙe-yaƙe a yankuna kamar Amhara, Oromia da Tigray ya jawo asarar rayuka da dama, tare da haddasa ƙaura da lalacewar tattalin arziki.

    Adhanom ya yi kira ga shugabanni su kwantar da hankali tare da rungumar hanyoyin siyasa domin samar da zaman lafiya.

  10. Sojojin Najeriya sun ce sun ceto fasinjoji 33 da aka sace a Zamfara

    Rundunar sojin Najeirya ta ce dakarunta na Operation Fansan Yamma sun ceto mutum 33 da 'yanbindiga suka yi garkuwa da su a ƙaramar hukumar Tsafe da ke jihar Zamfara, bayan samun sahihan bayanai kan sace fasinjojin da ke tafiya ta yankin Magazu.

    Sanarwar da jami'in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar ta ce sojojin tare da 'yan sanda a Tsafe sun samu bayanin lamarin ne da yammacin ranar 8 ga Agusta, 2026.

    Nan take dakarun suka nufi wurin da lamarin ya faru, inda suka ci karo da maharan suna tafiya da waɗanda suka sace zuwa wani wurin da ba a sani ba.

    Bayan an yi musayar wuta, maharan suka tsere cikin daji tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su.

    Rundunar ta ce an ceto dukkan fasinjojin 33 cikin koshin lafiya ba tare da samun asarar rai ba.

    A halin yanzu, dakarun na ci gaba da farautar maharan, yayin da kwamandan rundunar ya yaba wa jami'an bisa gaggawar daukar mataki tare da jaddada aniyar rundunar na kare rayuka da kuma tabbatar da tsaron manyan hanyoyin sufuri a yankin Arewa maso Yamma.

  11. Sabon Ƙawancen tsaron Saudiyya, Pakistan da Turkiyya ba barazana bace a gare mu - Iran

    Iran ta ce sabon ƙawancen tsaro tsakanin Saudiyya, Pakistan da Turkiyya, wanda ake kira Yarjejeniyar Makkah, ba barazana bace a gare ta, kuma babu dalilin da zai sa ta damu da wannan yarjejeniya.

    Mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana haka a taron manema labarai na mako-mako, yana mai cewa ƙasashen yankin sun fara fahimtar cewa ba za su iya dogaro da Amurka kaɗai wajen samar da tsaro ba.

    Ya kuma ce har yanzu mashigar Hormuz ba zai iya zama cikakkiyar hanyar jiragen dakon mai me aminci ba, muddin ana ci gaba da wasu matakan takunkumi da kuma saɓa yarjejeniyoyi da aka cimma.

    Baghaei ya ƙara da cewa Iran na maida hankali kan tattaunawa da Oman kan batutuwan da suka shafi Hormuz, yayin da ya jaddada cewa ƙasarsa ba ta wata tattaunawa kai tsaye da Amurka ba, sai dai ta hanyar masu shiga tsakani.

  12. INEC ta ƙara wa'adin miƙa sunayen ƴan takarar gwamna da majalisun jihohi

    Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta tsawaita wa'adin da jam'iyyun siyasa za su shigar da sunayen 'yan takararsu na zaɓen gwamna da na majalisun dokokin jihohi daga ranar 8 zuwa 11 ga Agustan 2026.

    INEC ta ce ta ɗauki matakin ne bayan roƙon da jam'iyyun siyasa suka yi na ƙarin lokaci domin kammala aikin miƙa bayanan 'yan takararsu.

    Haka kuma, hukumar ta dakatar da rabon katin zaɓe na dindindin (PVC) a Jihar Osun gabanin zaɓen gwamna da za a gudanar ranar 15 ga Agusta.

    INEC ta ƙara da cewa ta samar da sababbin katunan zaɓe ga wasu masu zaɓe a ƙananan hukumomin Odo-Otin da Ife Central bayan da wasu ɓata-gari suka sace katunan daga cibiyoyin rabonsu, tana mai jaddada cewa ba za a iya amfani da katunan da aka sace wajen kaɗa ƙuri'a ba.

  13. An fara shari'ar kisan Tupac Shakur bayan shekaru 30

    An fara shari’ar wani tsohon shugaban ƙungiyar daba, Duane “Keffe D” Davis, a Las Vegas kan zargin hannu a kisan fitaccen mawakin Amurka Tupac Shakur, wanda aka kashe a shekarar 1996.

    Masu gabatar da ƙara sun ce Davis ne ya shirya kisan tare da samar da bindigar da aka yi amfani da ita wajen harbin Tupac bayan wata takaddama tsakanin ƙungiyoyin da ke da alaƙa da kamfanonin waƙoƙi na gabashi da yammacin Amurka.

    Tupac, wanda ya yi fice da waƙoƙi kamar California Love da All Eyez on Me, ya mutu yana da shekara 25 bayan an harbe shi a Las Vegas bayan kallon damben Mike Tyson.

    Ana sa ran shari’ar za ta ɗauki kusan wata guda, kuma idan aka samu Davis da laifi, zai iya fuskantar hukuncin daurin rai da rai ba tare da beli ba.

  14. Nijar ta gayyaci kamfanonin sufuri bayan hatsarin bas da ya kashe mutum 22

    Gwamnatin Nijar ta gayyaci kamfanonin sufuri biyu domin amsa tambayoyi bayan wani mummunan hatsarin bas da ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 22, ciki har da sojoji 17.

    Ma'aikatar Sufurin ƙasar ta ce motocin kamfanonin STM da SONITRAV ne suka yi karo da juna gab da ƙauyen Rezi a yankin Madaoua.

    Motar kamfanin SONITRAV na ɗauke da sojojin da ke dawowa daga horaswa.

    Baya ga mutum 22 da suka rasu, mutum 37 sun kuma jikkata.

    Hukumomi sun ce sun fara bincike kan musabbabin hatsarin tare da ɗaukar matakan hana irin haka a gaba.

    Hatsarin ya sake tayar da hankali kan matsalar haɗurran motoci a hanya a Nijar, inda ake yawan danganta su da gudun da ya wuce kima, take dokokin hanya da kuma lodin da ya wuce ƙa'id

  15. Iran ta naɗa Mohsen Rezaei wakilin Mojtaba Khamenei a majalisar tsaron ƙasar

    Sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, a cikin wata wasiƙa da aka danganta da shi ya naɗa Mohsen Rezaei a matsayin wakilinsa a Majalisar Tsaron Ƙasar Iran.

    Sanarwar ta kuma yaba da gudunmawar Mohammad Baqer Zolghadr, wanda ake raɗe-raɗin zai sauka daga muƙaminsa na sakataren majalisar, tare da naɗa shi a matsayin mai ba da shawara kan harkokin siyasa.

    Baya ga Rezaei, Saeed Jalili ma wakilin Jagoran addini ne a majalisar, wadda Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ke jagoranta.

    A tsarin mulkin Iran, duk wani muhimmin ƙuduri na majalisar sai Jagoran ƙasar ya amince da shi kafin aiwatarwa.

    Mojtaba Khamenei, wanda ya gaji mahaifinsa bayan kashe shi, har yanzu bai bayyana a bainar jama'a ba, kuma saƙonnin da ake fitarwa da sunansa na rubuce ne kawai.

  16. Iran ta kwashe shekaru 51 tana nuna mugun hali - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Iran ta kwashe shekaru 51 tana nuna abin da ya kira “ɗabi’a mara kyau”.

    Trump ya bayyana hakan ne a shafinsa na Truth Social, inda ya wallafa jadawalin da ke nuna faduwar darajar kuɗin Iran, rial.

    A wani ɓangaren kuma, an naɗa Mohsen Rezaei a matsayin wakilin Jagoran Iran a Majalisar Tsaron Ƙasa ta Ƙoli, yayin da aka naɗa Shugaba Masoud Pezeshkian a matsayin sakataren majalisar.

    Haka kuma, babban hafsan sojojin Amurka ya ce tun bayan fara toshe harkokin ruwan Iran, sojojin ƙasar sun tilasta wa jiragen kasuwanci 55 sauya hanya, tare da tsayar da wasu jirage biyu ta hanyar harbe-harbe.

  17. 'Iran na ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa a mashigar Hormuz'

    Iran na ci gaba da kai hare-hare tare da tsaurara sa ido kan jiragen ruwa da ke bi ta mashigar Hormuz ba bisa ƙa'ida ba lamarin da ya sa Ƙungiyar Kula da Harkokin Teku ta Birtaniya (UKMTO) ta ce hare-haren na barazana ga zirga-zirgar jiragen daukon mai.

    A cikin sabon rahotonta na wata-wata, UKMTO ta bayyana cewa Iran ta kai hari kan wani tankar dakon mai na Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Asabar, abin da ya ƙara rage zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar zuwa kaɗan daga cikin jiragen da ke amfani da wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

    Haka kuma, ƙungiyar ta ce ana ci gaba da ayyukan soja kai tsaye, ciki har da hare-haren makamai masu linzami da fashe-fashe a kusa da jiragen ruwa a hanyoyin ruwa da ke kudancin mashigar zuwa ƙasar Oman.

    UKMTO ta kuma yi gargaɗin cewa har yanzu akwai nakiyoyin ruwa da ba a gano ko kuma ba a tarwatsa ba a yankin, lamarin da ke ci gaba da barazana ga tsaron jiragen ruwa da harkokin kasuwanci a mashigar Hormuz.

  18. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.