KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 10/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 10 ga watan Agustan 2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Diflomasiyya kaɗai ba za ta kawo ƙarshen rikicin mashigar Hormuz ba - Iran

    ..

    Asalin hoton, IRNA

    Iran ta ce ba za a iya kawo ƙarshen rikicin da ke tattare da mashigar Hormuz ta hanyar diflomasiyya kaɗai ba, tana mai jaddada cewa dole ne a haɗa tattaunawa da amfani da ƙarfin ƙasa wajen kare muradunta.

    Mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana cewa diflomasiyya na taka muhimmiyar rawa wajen kare bukatun ƙasar, amma ba za ta wadatar ba muddin akwai abin da ya kira matsin lamba da takunkumin ruwa da Amurka ke amfani da shi.

    A cewarsa, Iran na haɗa hanyoyin diflomasiyya da ƙarfin soja domin tunkarar ƙalubalen da take fuskanta, yana mai cewa wannan ne matakin da ƙasar ke ɗauka a halin yanzu.

    Ya kuma ce duk da ci gaban tattaunawar Iran da Oman kan tsara hanyar zirga-zirga a mashigar Hormuz, hakan ba yana nufin za a sake buɗe mashigin gaba ɗaya ga zirga-zirgar jiragen ruwa ba.

  2. Shugaban WHO ya buƙaci shugabannin Habasha su zaɓi tattaunawa maimakon yaƙi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban Daraktan Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), Tedros Adhanom, ya buƙaci shugabannin gwamnatin Habasha da na yankunan su nemi mafita ta hanyar tattaunawa maimakon amfani da ƙarfin soja wajen warware rikice-rikicen ƙasar.

    Ya ce ci gaba da yaƙe-yaƙe a yankuna kamar Amhara, Oromia da Tigray ya jawo asarar rayuka da dama, tare da haddasa ƙaura da lalacewar tattalin arziki.

    Adhanom ya yi kira ga shugabanni su kwantar da hankali tare da rungumar hanyoyin siyasa domin samar da zaman lafiya.

  3. Sojojin Najeriya sun ce sun ceto fasinjoji 33 da aka sace a Zamfara

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeirya ta ce dakarunta na Operation Fansan Yamma sun ceto mutum 33 da 'yanbindiga suka yi garkuwa da su a ƙaramar hukumar Tsafe da ke jihar Zamfara, bayan samun sahihan bayanai kan sace fasinjojin da ke tafiya ta yankin Magazu.

    Sanarwar da jami'in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar ta ce sojojin tare da 'yan sanda a Tsafe sun samu bayanin lamarin ne da yammacin ranar 8 ga Agusta, 2026.

    Nan take dakarun suka nufi wurin da lamarin ya faru, inda suka ci karo da maharan suna tafiya da waɗanda suka sace zuwa wani wurin da ba a sani ba.

    Bayan an yi musayar wuta, maharan suka tsere cikin daji tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su.

    Rundunar ta ce an ceto dukkan fasinjojin 33 cikin koshin lafiya ba tare da samun asarar rai ba.

    A halin yanzu, dakarun na ci gaba da farautar maharan, yayin da kwamandan rundunar ya yaba wa jami'an bisa gaggawar daukar mataki tare da jaddada aniyar rundunar na kare rayuka da kuma tabbatar da tsaron manyan hanyoyin sufuri a yankin Arewa maso Yamma.

  4. Sabon Ƙawancen tsaron Saudiyya, Pakistan da Turkiyya ba barazana bace a gare mu - Iran

    ....

    Asalin hoton, IRNA

    Iran ta ce sabon ƙawancen tsaro tsakanin Saudiyya, Pakistan da Turkiyya, wanda ake kira Yarjejeniyar Makkah, ba barazana bace a gare ta, kuma babu dalilin da zai sa ta damu da wannan yarjejeniya.

    Mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana haka a taron manema labarai na mako-mako, yana mai cewa ƙasashen yankin sun fara fahimtar cewa ba za su iya dogaro da Amurka kaɗai wajen samar da tsaro ba.

    Ya kuma ce har yanzu mashigar Hormuz ba zai iya zama cikakkiyar hanyar jiragen dakon mai me aminci ba, muddin ana ci gaba da wasu matakan takunkumi da kuma saɓa yarjejeniyoyi da aka cimma.

    Baghaei ya ƙara da cewa Iran na maida hankali kan tattaunawa da Oman kan batutuwan da suka shafi Hormuz, yayin da ya jaddada cewa ƙasarsa ba ta wata tattaunawa kai tsaye da Amurka ba, sai dai ta hanyar masu shiga tsakani.

  5. INEC ta ƙara wa'adin miƙa sunayen ƴan takarar gwamna da majalisun jihohi

    ...

    Asalin hoton, INEC

    Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta tsawaita wa'adin da jam'iyyun siyasa za su shigar da sunayen 'yan takararsu na zaɓen gwamna da na majalisun dokokin jihohi daga ranar 8 zuwa 11 ga Agustan 2026.

    INEC ta ce ta ɗauki matakin ne bayan roƙon da jam'iyyun siyasa suka yi na ƙarin lokaci domin kammala aikin miƙa bayanan 'yan takararsu.

    Haka kuma, hukumar ta dakatar da rabon katin zaɓe na dindindin (PVC) a Jihar Osun gabanin zaɓen gwamna da za a gudanar ranar 15 ga Agusta.

    INEC ta ƙara da cewa ta samar da sababbin katunan zaɓe ga wasu masu zaɓe a ƙananan hukumomin Odo-Otin da Ife Central bayan da wasu ɓata-gari suka sace katunan daga cibiyoyin rabonsu, tana mai jaddada cewa ba za a iya amfani da katunan da aka sace wajen kaɗa ƙuri'a ba.

  6. An fara shari'ar kisan Tupac Shakur bayan shekaru 30

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    An fara shari’ar wani tsohon shugaban ƙungiyar daba, Duane “Keffe D” Davis, a Las Vegas kan zargin hannu a kisan fitaccen mawakin Amurka Tupac Shakur, wanda aka kashe a shekarar 1996.

    Masu gabatar da ƙara sun ce Davis ne ya shirya kisan tare da samar da bindigar da aka yi amfani da ita wajen harbin Tupac bayan wata takaddama tsakanin ƙungiyoyin da ke da alaƙa da kamfanonin waƙoƙi na gabashi da yammacin Amurka.

    Tupac, wanda ya yi fice da waƙoƙi kamar California Love da All Eyez on Me, ya mutu yana da shekara 25 bayan an harbe shi a Las Vegas bayan kallon damben Mike Tyson.

    Ana sa ran shari’ar za ta ɗauki kusan wata guda, kuma idan aka samu Davis da laifi, zai iya fuskantar hukuncin daurin rai da rai ba tare da beli ba.

  7. Nijar ta gayyaci kamfanonin sufuri bayan hatsarin bas da ya kashe mutum 22

    ....

    Asalin hoton, AFP

    Gwamnatin Nijar ta gayyaci kamfanonin sufuri biyu domin amsa tambayoyi bayan wani mummunan hatsarin bas da ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 22, ciki har da sojoji 17.

    Ma'aikatar Sufurin ƙasar ta ce motocin kamfanonin STM da SONITRAV ne suka yi karo da juna gab da ƙauyen Rezi a yankin Madaoua.

    Motar kamfanin SONITRAV na ɗauke da sojojin da ke dawowa daga horaswa.

    Baya ga mutum 22 da suka rasu, mutum 37 sun kuma jikkata.

    Hukumomi sun ce sun fara bincike kan musabbabin hatsarin tare da ɗaukar matakan hana irin haka a gaba.

    Hatsarin ya sake tayar da hankali kan matsalar haɗurran motoci a hanya a Nijar, inda ake yawan danganta su da gudun da ya wuce kima, take dokokin hanya da kuma lodin da ya wuce ƙa'id

  8. Iran ta naɗa Mohsen Rezaei wakilin Mojtaba Khamenei a majalisar tsaron ƙasar

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, a cikin wata wasiƙa da aka danganta da shi ya naɗa Mohsen Rezaei a matsayin wakilinsa a Majalisar Tsaron Ƙasar Iran.

    Sanarwar ta kuma yaba da gudunmawar Mohammad Baqer Zolghadr, wanda ake raɗe-raɗin zai sauka daga muƙaminsa na sakataren majalisar, tare da naɗa shi a matsayin mai ba da shawara kan harkokin siyasa.

    Baya ga Rezaei, Saeed Jalili ma wakilin Jagoran addini ne a majalisar, wadda Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ke jagoranta.

    A tsarin mulkin Iran, duk wani muhimmin ƙuduri na majalisar sai Jagoran ƙasar ya amince da shi kafin aiwatarwa.

    Mojtaba Khamenei, wanda ya gaji mahaifinsa bayan kashe shi, har yanzu bai bayyana a bainar jama'a ba, kuma saƙonnin da ake fitarwa da sunansa na rubuce ne kawai.

  9. Iran ta kwashe shekaru 51 tana nuna mugun hali - Trump

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Iran ta kwashe shekaru 51 tana nuna abin da ya kira “ɗabi’a mara kyau”.

    Trump ya bayyana hakan ne a shafinsa na Truth Social, inda ya wallafa jadawalin da ke nuna faduwar darajar kuɗin Iran, rial.

    A wani ɓangaren kuma, an naɗa Mohsen Rezaei a matsayin wakilin Jagoran Iran a Majalisar Tsaron Ƙasa ta Ƙoli, yayin da aka naɗa Shugaba Masoud Pezeshkian a matsayin sakataren majalisar.

    Haka kuma, babban hafsan sojojin Amurka ya ce tun bayan fara toshe harkokin ruwan Iran, sojojin ƙasar sun tilasta wa jiragen kasuwanci 55 sauya hanya, tare da tsayar da wasu jirage biyu ta hanyar harbe-harbe.

  10. 'Iran na ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa a mashigar Hormuz'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran na ci gaba da kai hare-hare tare da tsaurara sa ido kan jiragen ruwa da ke bi ta mashigar Hormuz ba bisa ƙa'ida ba lamarin da ya sa Ƙungiyar Kula da Harkokin Teku ta Birtaniya (UKMTO) ta ce hare-haren na barazana ga zirga-zirgar jiragen daukon mai.

    A cikin sabon rahotonta na wata-wata, UKMTO ta bayyana cewa Iran ta kai hari kan wani tankar dakon mai na Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Asabar, abin da ya ƙara rage zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar zuwa kaɗan daga cikin jiragen da ke amfani da wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

    Haka kuma, ƙungiyar ta ce ana ci gaba da ayyukan soja kai tsaye, ciki har da hare-haren makamai masu linzami da fashe-fashe a kusa da jiragen ruwa a hanyoyin ruwa da ke kudancin mashigar zuwa ƙasar Oman.

    UKMTO ta kuma yi gargaɗin cewa har yanzu akwai nakiyoyin ruwa da ba a gano ko kuma ba a tarwatsa ba a yankin, lamarin da ke ci gaba da barazana ga tsaron jiragen ruwa da harkokin kasuwanci a mashigar Hormuz.

  11. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.