Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 31/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 31 ga watan Yulin 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed da Abdullahi Bello

  1. Ghana ta amince da ƙudurin mayar da mulkin ƙasar shekara biyar

    Gwamnatin Ghana ta amince da wasu muhimman gyare-gyare da kwamitin yi wa kundin mulkin ƙasar garambawul ya gabatar, ciki har da tsawaita wa'adin mulkin shugaban ƙasa da na 'yan majalisa daga shekara huɗu zuwa shekara biyar, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na cikin ƙasar suka ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

    Babban Lauyan Ƙasa kuma Ministan Shari'a, Dominic Aniye, ya ce: "Muna tunanin waɗannan zauye-zauyen za su yi. A ƙarƙashin tsarin wa'adin shekara huɗu na yanzu, watannin farko na kowane zangon mulki suna wucewa ne wajen karɓar mulki, sannan shekarar ƙarshe ta shige cikin shirye-shiryen zaɓe."

    Ya ƙara da cewa: "Wa'adin shekara biyar zai ba kowace gwamnati isasshen lokaci wajen tsara manufofi, aiwatar da su da kuma tantance sakamakonsu."

    Kwamitin ya miƙa rahotonsa na ƙarshe ga Shugaba John Mahama, inda ya ba da shawarar a yi wa kundin tsarin mulkin shekarar 1992 kwaskwarima.

    Gwamnatin ta kuma amince da wasu shawarwari da suka haɗa da:

    • Ƙara yawan kujerun majalisa daga 276 zuwa 300.
    • Rage mafi ƙarancin shekarun da ake buƙata domin tsayawa takarar shugaban ƙasa daga 40 zuwa 35.

    Sauran shawarwarin sun haɗa da:

    • Soke hukuncin kisa.
    • Taƙaita yawan ministoci zuwa 60 kacal.
    • Soke cikakken keɓewar shugaban ƙasa daga biyan haraji.
    • Taƙaita adadin alƙalan Kotun Ƙoli zuwa 19.
    • Samar da wa'adi guda ɗaya na shekara 10 ga Babban Alƙalin Ƙasa ba tare da damar sake naɗa shi ba.

    Ana sa ran za a gabatar da ƙudirin gyaran kundin tsarin mulkin nan da watan Oktoba, yayin da ake sa ran gudanar da ƙuri'ar raba gardama kan sauye-sauyen a shekarar 2027.

  2. 'Waɗanda suka sace ɗaliban Oyo sun buƙaci musaya da manyansu muka ƙi'

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya ce gwamnati ta ƙi amincewa da buƙatun masu garkuwa da mutanen da suka kai hari makarantu uku a jihar Oyo da ke kudu maso yammacin ƙasar a ranar 15 ga Mayu.

    Maimakon haka, gwamnati ta mayar da hankali kan aikin ceto ɗaliban ne ta hanyar amfani da bayanan sirri, kamar yadda shafin jaridar Punch ya ruwaito a ranar 31 ga Yuli.

    Tinubu ya bayyana haka ne a karon farko tun bayan da aka ceto aƙalla ɗalibai da malamai 39 a ranar 10 ga Yuli, yayin wata ganawa da tawagar sarakunan gargajiya daga jihar Oyo a Abuja.

    Ya ce: "Mun ƙi tattaunawa kan biyan kuɗin fansa. Waɗannan masu aikata laifin sun buƙaci mu saki wasu daga cikin 'yan ƙungiyoyinsu da aka riga aka kama. Wannan na daga cikin sharuɗɗansu, baya ga kuɗin da suke nema."

    Ya ƙara da cewa: "Mun ce babu wata yarjejeniya. Ba za mu tattauna da masu aikata laifi ba. Sun aikata kisan kai, kuma mun shirya murƙushe su. Suna da iyalai da kuma al'ummomin da suka fito."

    Har ila yau, Tinubu ya danganta ƙaruwar sace-sacen mutane da hare-haren masu tayar da ƙayar baya a Najeriya da matsalolin tsaro da ke ƙasashen yankin Sahel.

  3. Mawaƙiyar Afirka ta Kudu Tyla ta fasa zuwa Najeriya taron kalankuwa

    Mawaƙiyar Afirka ta Kudu, Tyla, ta cire Najeriya a cikin jerin ƙasashen da za ta je domin taron kalankuwa da ta shirya gudanarwa a ƙasashen duniya da dama.

    Ta shirya zuwa ƙasashen ne domin baje-kolin waƙoƙin sabon kundin waƙokinta.

    Sai dai alamu sun nuna ta fasa zuwa Najeriya bayan ce-ce-ku-ce da suka biyo bayan nuna wariyar baƙi a ƙasarta ta Afirka ta Kudu.

    A ranar Litinin ne Tyla ta sanar da ranakun rangadin , kuma a ciki ranaku uku na wasanni a nahiyar Afirka.

    Da farko dai an tsara za ta raƙashe ne a a Legas ranar 22 ga Disamba ne.

  4. Dubban baƙin-haure sun tsallaka Spain ta Morocco

    Dubban ƙarin baƙin haure sun taru a kan bakin iyakar Ceuta, yankin Sifaniya da ke Arewacin Afirka, bayan da yankin ya fuskanci gagarumar kwararar masu shiga ƙasar a jiya Alhamis, karo na farko cikin shekara biyar.

    Gwamnatin Sifaniya ta tura karin sojoji domin taimakawa wajen shawo kan lamarin, yayin da ake sa ran Firaminista Pedro Sánchez zai kai ziyara yankin na Ceuta a yau Juma'a.

    Rahotanni sun ce hukumomin Maroko sun fara ɗaukar tsauraran matakai kan bakin hauren, inda a daren da ya gabata suka rika fesa wa bakin ruwa domin tarwatsa su.

    Sifaniya ta ce ta cimma yarjejeniya da Maroko domin mayar da bakin hauren zuwa ƙasarsu cikin gaggawa.

    Sai dai har yanzu babu wata sanarwa daga gwamnatin Maroko a kan batun. Jami'ai a Ceuta sun ce aƙalla mutum 15 sun mutu bayan da suka nutse a teku yayin da suke ƙoƙarin isa yankin na Sifaniya.

  5. Kotu ta ba ƴansandan Brazil izinin binciken ɗan shugaban ƙasar

    Wani alƙalin Kotun Koli ta Brazil ya bayar da izini ga ƴansanda su gudanar da binciken kan Fabio Lula da Silva, babban ɗan Shugaba Luiz Inácio Lula da Silva, bayan an danganta shi da wata badaƙalar zamba da ta shafi maƙudan kuɗaɗe.

    Ana zargin Fabio, wanda aka fi sani da Lulinha, da taimaka wa wani mai rajin neman tasiri a harkokin gwamnati da ke zaman kurkuku a yanzu, a mu'amalolinsa da Ma'aikatar Lafiya ta Brazil dangane da kasuwancin tabar wiwi da ake amfani da ita wajen magani.

    Mutumin da ake magana a kansa an same shi da laifin damfarar ƴan fansho a wata shari'a ta daban a bara, kuma tuni an taɓa binciken Lulinha dangane da wannan batu.

    Lauyoyin Fabio Lula da Silva sun shaida wa kafafen yaɗa labarai na Brazil cewa ba za su iya yin tsokaci kan sabon binciken ba, domin har yanzu ba su ga cikakkun bayanansa ba.

    Shugaba Lula ya sha alwashin cewa ba za a nuna sani ko sabo ba a kan dan nasa.

  6. Hamas ta amince ta ajiye makami a Gaza bayan tattaunawa da Trump

    Bayan tattaunawar wata da watanni, ƙungiyar Hamas ta ce ta amince da wani shiri da Hukumar Zaman Lafiya ta Shugaban Amurka Donald Trump ta gabatar, na ta kwance damarar yaki gaba daya - ta ajiye makamanta a Zirin Gaza.

    Trump ya bayyana yarjejeniyar a matsayin babban abin tarihi, yana mai cewa ta zama wani muhimmin mataki na samar da sabuwar gwamnatin Falasɗinawa a Gaza.

    Wakilin BBC a Gaza, wanda ke birnin Alkahira na Masar, ya ce shirin ya tanadi ƙididdige da adana manyan makaman Hamas da suka rage ƙarƙashin kulawar hukumomin Falasɗinawa.

    Wakiliyar BBC ta ce, zuwa yanzu Isra'ila ba ta ce komai ba. Shugaba Trump dai ya ce dakarun Isra'ila za su fice daga Gaza da zarar an kammala kwance damarar Hamas da sauran ƙungiyoyin da ke ɗauke da makamai.

  7. Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa, barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'atu babbar rana.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.