Amurka ta ce ta kai hari kan kusan wurare dubu 6 a cikin Iran
Amurka ta ce ta kai hare-hare kan kusan wurare dubu shida a cikin Iran tun bayan fara yaƙi da ƙasar.
Ta ce hare-haren sun haɗa da kai farmaki kan gomman jiragen ruwa, wuraren kera makamai, da kuma kan garkuwar kare hare-haren sama.
A halin da ake ciki kuma, Isra’ila ta ce tana kai wasu sababbin jerin hare-hare ta sama kan babban birnin Iran ɗin, Tehran.
A daren da ya gabata ma, Isra’ilar ta ce ta kai wani hari a wani wuri da ke da alaƙa da kera makaman nukiliya.
Sai dai Iran ta dage cewa shirinta na nukiliya ba na kera makamai ba ne, yana da nufin ayyukan ci gaban ƙasa na zaman lafiya.
An kai waɗannan hare-haren na baya-bayan nan ne yayin da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ke cewa ƙasarsa na yi wa rundunar sojin juyin juya hali ta Iran gagarumar illa.