Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/11/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza da Muhammad Annur Muhammad

  1. Dan takarar LP, Olorunfemi ya kaɗa ƙuri'arsa

    Dan takarar gwamnan na jam'iyyar LP, Festus Ayo Olorunfemi ya kaɗa ƙuri'arsa.

    Olorunfemi ya kaɗa ƙuri'arsa a rumfar zaɓe mai lamba 8, a ƙaramar hukumar Akoko North West da ke jihar.

    A ranar Juma'a ne hukumar zaɓen ƙasar INEC ta sanya sunansa cikin jerin 'yan takara bayan hukuncin wata kotu da ya buƙaci a sauya Olusola Ebiseni.

  2. Jami'an DSS sun kama wanda ake zargi da sayen ƙuri'a da jakankunan kuɗi

    Jami'an hukumar tsaro ta DSS a Najeriya sun kama wani mutum da ake zargi da sayen ƙuri'a a zaɓen gwaman jihar Ondo.

    Gidan talbijin na Channels ya ruwaito cewa jami'an na DSS sun kama mutumin da jakankunan kuɗi da ake kyautata zaton zai yi amfani da su wajen sayen ƙuri'a.

    An dai kama mutumin a rumfar zaɓe mai lamba ta 007 da ke makarantar furamaren St. Stephen a birnin Akure.

  3. Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya kaɗa ƙuri'arsa

    Gwamnan jihar Ondo kuma ɗan takarar jam'iyyar APC mai mulkin jihar, Lucky Aiyedatiwa ya kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen.

    Mista Aiyedatiwa ya kaɗa ƙuri'arsa na rumfar zabensa da ke yankin ƙaramar hukumar Ilaje.

    A watan Disamban bara ne aka rantsar da Aiyedatiwa a matsayin gwamnan jihar bayan rasuwar tsohon gwamna marigayi Rotimi Akeredolu.

  4. Jami'an EFCC na sanya idanu kan masu sayen ƙuri'a a zaɓen

    Jami'an hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya, EFCC na sanya idanu kan masu yunkurin sayen ƙuri'a a zaɓen gwaman Ondo da ke gudana.

    Galibi a wasu zaɓukan Najeriya akan samu rahotonnin sayen ƙuri'un masu zaɓe daga wakilan jam'iyyun daban-daban.

    Jami'an na ta zagaya rumfunan zaɓen domin lura da wannan ɗabi'a.

  5. Mafi yawan tititan birnin Akure sun kaance fayau babu zirga-zirga

    Titinan Akure babban birnin jihar Ondo sun kasance fayau babu zirga-zirgar ababen hawa a yayin da ake gudanar da zaɓen gwamna a faɗin jihar.

    Wakilin BBC da ya zagaya wasu sassan birnin ya ce mafi yawan titinan babu zirga-zirgar ababen hawa.

    Dama dai babban sifeton 'yansandan ƙasar ya sanya dokar taƙaita zirga-zirga a faɗin jihar a ranar zaɓen daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa 6:00 na maraice.

    A cikin sanarwar dokar, babban sifeton 'yansandan ya ce dole ne kowa ya yi biyayya ga dokar, in ban da masu ayyuka na musamman kamar jami'an lafiya da 'yanjarida.

  6. An amfani da na'urar BVAS domin tantance masu zaɓe

    Ana amfani da na'urorin tantance masu zaɓe ta BVAS a zaɓen na jihar Ondo.

    Wakilin BBC ya ce an samu fitowar tsofaffin mutane cike da zumuɗin zuwa rumfunan zaɓe domin kaɗa ƙuri'unsu.

    Masu zaɓen sun ce sun yi imanin za su iya kawo wa kansu duka sauyin da suke so ne ta hanayr ƙuri'unsu.

  7. An fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan jihar Ondo

    Masu zaɓe a jihar Ondo sun fara kaɗa ƙuri'a domin zaɓen sabon gwamnan jihar.

    Kawo yanzu zaɓen na gudana cikin kwanciyar hankali da lumana a wasu sassan birnin Akure da wakiin BBC ya zagaya.

    Ana sa ran kammala kaɗa ƙuri'a da misalain ƙarfe 2:30 na rana, bayan duka mutanen da ke kan layin zaɓe a daidai wannan lokaci sun kammala jefa ƙuri'arsu.

    AJam'iyyu 18 ne ke fafatawa a zaɓen, sai dai ana ganin takarar za ta fi zafi ne tsakanin gwaman jihar Lucky Aiyedatiwa na APC da Agboola Ajayi na PDP.

  8. Abu huɗu da suka kamata ku sani game da zaɓen jihar Ondo

    A yau Asabar ne ake gudanar da zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke yankin kudu maso yammacin Najeriya.

    Jihar Ondo na daga cikin jihohin ƙasar da ba a gudanar da zaɓukansu lokaci guda da na sauran jihohi.

    Hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta ce mutum miliyan 2,053,061 ne suka yi rajistar zaɓe a faɗin jihar, yayin da matasa ke da kashi 35.41 cikin 100 na waɗanda suka yi rajistar zaɓen.

    Ga wasu abubuwa guda huɗu da suka kamata ku sani dangane da zaɓen na jihar Ondo na yau Asabar.

  9. An fara tantance masu kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan jihar Ondo

    Masu kaɗa ƙuri'a a jihar Ondo da ke yankin kudu maso yammacin Najeriya, sun hau kan layin zaɓe domin zaɓen sabon gwamnan jihar.

    Tuni dai malaman zaɓe suka isa wasu rumfuna zaɓen a kan lokaci, kamar yadda wakiln BBC da ya zagaya wasu rumfunan zaɓen da ke Akure babban birnin jihar ya tabbatar.

    Malaman zaɓen sun fara tantance masu kaɗa ƙuri'a waɗanda suka hau kan layi, domin gudanar da zaɓen.

  10. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, fatan kun wayi gari lafiya.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wanan lokaci, domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a Najeriya, da sauran sassan duniya, musamman kan zaɓen gwamnan jihar Ondo.

    Ku biyo mu a shafukan sada zumunta don tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.