Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi na kawo muku sahihan bayanai dangane da wainar da ake toyawa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR da Abdullahi Bello

  1. Lebanon da Isra'ila za su yi ganawar gaba da gaba a karon farko

    Ana sa ran jakadan Isra'ila da na Lebanon a Amurka su shiga tattaunawa ta gaba da gaba a Washington naN gaba.

    Wannan shi ne karon farko a cikin gomman shekaru, inda jami'ai daga kasashen biyu - wadanda ba su da alaka ta diflomasiyya, z asu yi hakan.

    Hukumomin Lebanon farko na son su ga an dakatar da bude wuta a yakin da Isra'ila ke yi da kungiyar Hezbollah, wadda Iran ke mara wa baya, to amma kuma Isra'ila ta ce ba wannan magana, dole ne sai Hezbollah, ta zubar da makamanta.

    Shi ma sakataren harkokin waje na Amurka Marco Rubio zai halarci tattaunawar. Hezbollah ta kafe lalle cewa Lebanon ta fice daga wannan sha'ani.

    A jiya Litinin shugaban kungiyar Naim Qassim, ya kara jaddada, matsayar kungiyar ta kawar da yuwuwar tattaunawa ta kai tsaye da Isra'ila

  2. Mataimakin shugaban Amurka, JD Vance ya zargi Iran da "ta'addanci na tattalin arziƙi"

    Mataimamin shugaban Amurka JD Vance ya zargi gwamnatin Iran da abin da ya kira ta'addanci na tattalin arziki saboda rufe mashigar Hormuz ta hana jiragen ruwa bi.

    Ya ce Shugaba Trump ya nuna - kamar yadda ya ce - shi ma kwallo ne - a kan wannan harka.

    A jiya Litinin Amurka ta fara aiwatar da abin da ta kira - datse jiragen ruwa ta hana su amfani da tasoshin ruwa na Iran.

    Ya zargi Irn da tsilla-tsilla a lokacin tattaunawar ta karshen mako , inda ya ce yana sa ran Iran ta bude mashigar gaba daya, ita kuma a saka mata da dakatar da bude wuta.

    Hakan dai ya biyo bayan gaza cimma matsaya a tattaunawar zaman lafiya ta Iran da Amurka a Pakistan.

    Amma kuma duk da haka mataimakin shugaban na Amurka ya sheda wa kafar yada labarai ta Amurka Fox News cewa an samu cigaba sosai a tattaunawar.

  3. Buɗewa

    Masu bibiyar shafin Hausa kai tsaye da ke kawo muku labarai da rahotannin al'amuran da ke faruwa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sassan duniya musamman Najeriya wadda ita ce ƙasa mafi girma da yawan baƙar fata a faɗin duniya.

    Kamar kullum ma yau za mu kawo muku bayanai dangane da irin wainar da ake toyawa a waɗannan wurare.

    Da fatan za ku kasance da shafin da ma sauran shafukan sada zumunta na BBC Hausa kamar Facebook da Instagram da X da kuma Youtube.