Lebanon da Isra'ila za su yi ganawar gaba da gaba a karon farko
Ana sa ran jakadan Isra'ila da na Lebanon a Amurka su shiga tattaunawa ta gaba da gaba a Washington naN gaba.
Wannan shi ne karon farko a cikin gomman shekaru, inda jami'ai daga kasashen biyu - wadanda ba su da alaka ta diflomasiyya, z asu yi hakan.
Hukumomin Lebanon farko na son su ga an dakatar da bude wuta a yakin da Isra'ila ke yi da kungiyar Hezbollah, wadda Iran ke mara wa baya, to amma kuma Isra'ila ta ce ba wannan magana, dole ne sai Hezbollah, ta zubar da makamanta.
Shi ma sakataren harkokin waje na Amurka Marco Rubio zai halarci tattaunawar. Hezbollah ta kafe lalle cewa Lebanon ta fice daga wannan sha'ani.
A jiya Litinin shugaban kungiyar Naim Qassim, ya kara jaddada, matsayar kungiyar ta kawar da yuwuwar tattaunawa ta kai tsaye da Isra'ila