BBC ta buɗe damar shiga domin neman kyautar lambar yabo ta Komla Dumor na hazaƙan ƴan jarida na Afirka, a karo na 10.
Ƴan jarida daga dukkan sassan Afirka ne za su iya shiga domin shiga neman lashe lambar yabon, wanda aka assasa domin ganowa da kuma ƙarfafa gwiwar haziƙan ƴan jarida daga nahiyar.
Wanda ya lashe kyautar zai shafe watanni uku a babban ofishin BBC da ke Landan, inda zai samu ƙwarewa da gogewa.
Za a rufe karɓar shiga gasar a ranar 20 ga Maris da misalin ƙarfe 23:59 GMT.
An samar da lambar yabon ne domin karrama Komla Dumor, fitaccen mai gabatar da shirye-shirye na BBC ɗan asalin ƙasar Ghana, wanda ya rasu yana da shekara 41, shekara 11 da suka gabata.
Matar Dumor, Kwansema Dumor, ta ce tana alfahari da irin tasirin da mijinta ya yi a BBC, sannan ta ce suna suna godiya ga BBC da take tunawa da gudunmuwar shi ta hanyar assasa karramawar.
BBC na ƙarfafa gwiwar ƴan jarida a faɗin Afirka da su shiga gasar, wadda ke neman bunƙasa da kuma karrama fitattun ƴan jarida da ke rayuwa tare da aiki a nahiyar.
Baya ga samun horo, wanda ya samu nasarar lashe kyautar, zai samu damar tafiya zuwa wata ƙasa a Afirka domin yin rahoto kan wani labari, wanda za a yaɗa a BBC ga masu bibiyar ta a faɗin duniya.
Shahararren ɗan jarida mai fafutuka, da kuzari, na da jajircewa wurin bayar da sahihan rahotonni kan labaran Afirka baki ɗaya, Dumor ya yi matuƙar tasiri a Afirka da sauran ƙasashen duniya.
BBC ta ƙuduri aniyar ci gaba da tunawa da shi ta hanyar bai wa ƴan jarida daga Afirka damar bayar da labarai daga Afirka don isa ga masu sauraro da ke faɗin duniya.
Rukia Bulle ce ta lashe kyautar a shekarar da ta gabata.
A lokacin da take samun horo a BBC, ƴar jaridar ta je ƙasar Senegal inda ta yi rahoto kan Baye Fall, domin fahimtar da duniya yanayin yadda suke gudanar da ibadarsu.
Babban daraktan sashen labarai, kuma mataimakin babban jami'in gudanarwa na BBC, Jonathan Munro ya ce, "muna farin cikin sanar da buɗe shiga wannan karramarwar ta Komla Dumor ta bana.
"Wannan ne karo na 10 na bayar da wannan kambun domin karrama hazaƙan ƴan jarida na Afirka da suka yi rahotanni masu tasiri daga nahiyar.
"Waɗanda suka lashe kyautar a baya, sun nuna basira da ƙwarewa matuƙa, don haka nake farin cikin sanar da buɗe na wannan shekarar domin samun sabon angon kyautar.
Dumor ya kasance mai gabatar da shirin Focus on Africa, shirin labarai na gidan talabijin na BBC na farko da ake yaɗa shi a kullum cikin harshen Ingilishi ga masu sauraro a Afirka. An watsa shi a tashar Labaran Duniya na BBC, wanda a shekarar da ta gabata ya haɗe da tashar yaɗa labarai ta BBC don samar da labaran talabijin na tsawon sa'o'i 24.
Ya kuma kasance ɗaya daga cikin jagororin masu gabatar da shirye-shirye na shirin safe na Turai a BBC.
Ya fara aiki a BBC ne a shekara ta 2007 bayan ya shafe shekara 10 yana aikin jarida a ƙasarsa Ghana inda ya lashe kyautar gwarzon ɗan jarida na Ghana.
A tsakanin shekarar 2007 zuwa 2009 ya gabatar da shirin 'Network Africa' a sashen ƙasa da ƙasa na BBC, kafin ya shiga shirin 'The World Today'.
A shekarar 2009 Dumor ya zama mai gabatar da labaran kasuwanci na Afirka na farko a shirin Labaran Duniya na BBC, Mai suna 'Africa Business Report'. Ya karaɗe nahiyar Afirka, inda ya gana da manyan ƴan kasuwar nahiyar, ya kuma bayar da rahotanni kan sabbin hanyoyin kasuwanci a Afrika.
A shekarar 2013 mujallar New African ta sanya Dumor a cikin jerin ƴan Afirka 100 wanda suka fi tasiri a nahiyar.
Waɗanda suka lashe kyautar a baya
-
2024: Rukia Bulle daga Kenya
-
2023: Paa Kwesi Asare daga Ghana
-
2022: Dingindaba Jonah Buyoya daga Zambia
-
2020: Victoria Rubadiri daga Kenya
-
2019: Solomon Serwanjja daga Uganda
-
2018: Waihiga Mwaura daga Kenya
-
2017: Amina Yuguda daga Najeriya
-
2016: Didi Akinyelure daga Najeriya
-
2015: Nancy Kacungira daga Uganda