KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 02 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. A wajenmu, duk wata barazana muna ɗaukarta da gaske - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ce tana ɗaukar duk wata barazana da ake yi mata a matsayin ta gaske kuma mai muhimmanci, duk kuwa da cewa wasu daga cikinsu na iya kasancewa wani ɓangare na yaɗa tsoro.

    Mukaddashin Ministan Tsaron Iran, Majid Ibn Reza, ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce daga babu wata barazana da Iran za ta yi watsi da ita ko a ɗauka da wasa.

    Ya ƙara da cewa Iran ba ta mamakin irin waɗannan barazanar kuma ba ta zama cikin sakaci, sai dai tana amfani da su wajen ƙara ƙarfafa shirinta na tsaro, da matakan kariya da kuma ƙarfin daƙile hare-hare.

    Kalaman nasa na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ya dakatar da shirin kai hari kan Iran a halin yanzu, bayan buƙatun da Iran da wasu ƙasashen yankin suka yi domin ba da damar warware rikicin ta hanyar tattaunawa.

  2. Na dakatar da harin Iran ne da sharaɗin cimma yarjejeniya cikin gaggawa - Trump

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya amince da dakatar da wani hari da aka shirya kai wa Iran bayan buƙatar da Iran da wasu ƙasashen Gabas ta Tsakiya suka yi, bisa sharaɗin cewa ɓangarorin za su cimma yarjejeniya cikin gaggawa.

    Trump ya bayyana a shafinsa na sada zumunta cewa an riga an amince da babban tsarin yarjejeniyar, wanda ya haɗa da buɗe mashigar Hormuz gaba ɗaya nan take da kuma kawo ƙarshen abin da ya kira barazanar shirin nukiliyar Iran.

    Ya ce Amurka ta kasance cikin cikakken shiri na kai hari kan Iran, tana kuma da ƙarfin soji da ya ce ba a ga irinsa ba tun bayan Yaƙin Duniya na Biyu.

    Trump ya ƙara da cewa Isra’ila ma ta amince da kauce wa kai hare-hare, tare da kira ga dukkan ɓangarorin da su gaggauta kammala yarjejeniyar.

  3. NDLEA ta daƙile yunƙurin fitar da hodar iblis zuwa China da Italiya ta Legas

    ...

    Asalin hoton, NDLEA/X

    Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta ce ta daƙile wani yunkuri na safarar hodar iblis zuwa ƙasashen China da Italiya bayan jami’anta sun gano ƙwayoyin da aka ɓoye a cikin turmin gargajiya da kuma wata jaka da aka shirya fitarwa ta wani kamfanin jigilar kaya a Legas.

    Hukumar ta ce hodar iblis ɗin da ake yunƙurin fitarwa zuwa China ta kai gram 250, yayin da wadda ake son aikawa Italiya ta kai gram 500.

    NDLEA ta ce jami’anta sun gano kayan ne a wani bincike da suka gudanar a ranar 30 ga Yulin 2026.

    A wani samame ta daban a jihar Rivers, hukumar ta kama wani fitaccen dillalin miyagun ƙwayoyi mai suna Ugo Gift Okonkwo, mai shekara 38, a yankin Eagle Island da ke Fatakwal.

    An ce an same shi da tabar wiwi, hodar iblis, methamphetamine, tramadol da kuma syrup ɗin codeine.

    Haka kuma a jihar Anambra, jami’an NDLEA sun tare wata mota ɗauke da kwalabe 26,000 na syrup ɗin codeine tare da cafke direbanta.

    Haka kuma, hukumar ta ce ta kama wani mutum mai shekara 27, a jihar Zamfara da ƙwayoyin tramadol 7,400 da ake zargin an tanade su ne domin kai wa ’yan bindiga.

  4. Aƙalla Falasɗinawa takwas sun mutu bayan hare-hare a Gaza

    Gaza

    Asalin hoton, Khames Alrefi/Anadolu via Getty Images

    Jami’n tsaron farin hula na Gaza sun ce aƙalla Falasɗinawa takwas ne suka mutu a hare-haren sama da aka kai cikin dare, waɗanda suka lalata gine-ginen gidaje.

    A cewar jami’an hukumar, biyu daga cikin waɗanda suka mutu namiji ne da mace, bayan wani jirgin yaƙin sama mai saukar ungulu na Isra’ila ya kai hari kan ginin gidansu da ke kudancin birnin Deir el-Balah.

    Hare-haren sun zo ne bayan ƙungiyar Hamas – wadda ta daɗe tana kasancewa babbar ƙungiyar da ke iko a Gaza – ta ce ta amince da sabon matakin yarjejeniyar da Shugaba Donald Trump ke jagoranta domin kawo ƙarshen yaƙin.

    Sai dai kakakin rundunar sojin Isra’ila ya ce hare-haren sun kasance ne kan mayaƙan da suke gudanar da ayyukan soji a Gaza.

  5. Ba za mu saki muryar Mojtaba Khamenei ba saboda ƴan leƙen asiri - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ce ba za ta saki sautin muryar sabon jagoran addinin ƙasar, Mojtaba Khamenei ba saboda fargabar cewa ƴan leƙen asiri za su iya amfani da ita wajen gano muhimman bayanan tsaro da suka shafe shi.

    A wani nazari da jaridar Hamshahri ta wallafa, ta bayyana cewa sautin murya na iya bayyana bayanai game da wurin da aka yi rikodi ta hanyar nazartar amo, girman ɗaki da kuma yanayin sauti na muhalli.

    Jaridar ta kuma ce ana iya amfani da sauye-sauyen da ke faruwa a mitar wutar lantarki da kuma siffofin na'urar da aka yi rikodin da ita wajen gano ƙasa, lokaci da ma takamaiman yankin da aka yi rikodin sautin.

    Tun bayan naɗin Mojtaba Khamenei a matsayin jagoran addinin Iran na uku, ba a gan shi a bainar jama'a ba, kuma ba a fitar da wani sabon hoto ko sautin muryarsa ba. Abin da aka wallafa zuwa yanzu dai shi ne saƙonnin rubuce-rubuce da ake dangantawa da shi ta kafafen yaɗa labaran Iran.

  6. Girgizar ƙasa ta afku sau biyu a lardin Khuzestan na Iran

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ruwaito cewa girgizar ƙasa ta afku sau biyua lardin Khuzestan tun daga safiyar Lahadi.

    A cewar kamfanin dillancin labaran Mehr, girgizar ƙasar ta farko mai ƙarfin maki 3.1 ta auku da misalin ƙarfe 3:13 na asubahin yau a kusa da garin Saland.

    Daga bisani kuma, da misalin ƙarfe 5:52 na safiya agogon yankin, an sake samun wata girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 3.5 a kusa da yankin Qala-e-Tal.

    Ya zuwa yanzu, babu wani rahoto da ya nuna asarar rayuka ko ɓarnar dukiya sakamakon girgizar ƙasar.

  7. A shirye muke mu mayar da martani mai tsauri ga duk wani hari - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana cewa ƙasarsa a shirye take ta mayar da martani mai ƙarfi ga duk wani hari da za a kai mata, yayin da ya yi gargaɗi ga Amurka kan duk wata “kasada” da za ta iya ƙara tayar da rikici a yankin.

    Araghchi ya bayyana hakan ne a tattaunawar waya da ya yi da ministan harkokin wajen Turkiyya da kuma babban kwamandan sojojin Pakistan, inda ya jaddada cewa Iran za ta kare kanta idan aka kai mata hari.

    Haka kuma ya shaida wa ministan harkokin wajen Saudiyya cewa duk wani hari da Amurka ko Isra’ila za su kai, ko kuma wanda wasu ƙasashen yankin za su goyi baya, zai fuskanci martani mai tsauri daga Iran.

    Wannan na zuwa ne yayin da rahotanni ke nuna yiwuwar Amurka ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Iran, yayin da ofisoshin jakadancin Amurka a Bagadaza da Erbil suka gargadi ‘yan ƙasarsu da su kasance cikin shirin ficewa daga yankin Gabas ta Tsakiya idan buƙatar hakan ta taso.

  8. Sojojin Najeriya sun kama wasu da ake zargi da kai wa dakarunsu hari a Delta

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta ƙarƙashin rundunar Operation UDOKA sun sanar da kama wasu manyan mambobin wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ake zargi da kai wa sojoji kwanton ɓauna a ranar 4 ga Mayun 2026 a jihar Delta.

    Harin ya yi sanadin mutuwar soja ɗaya tare da jikkata wani.

    A wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce bayan harin ne sojoji suka ƙaddamar da jerin samame bisa bayanan sirri domin kamo waɗanda suka aikata laifin da kuma ƙwato makaman da aka sace.

    Hakan ya kai ga cafke waɗanda ake kira Chiboy, Marathon da Onowu bayan sun tsere zuwa garin Oleh da ke jihar Delta.

    Sojojin sun ce waɗanda aka kama sun jagorance su zuwa maɓoyarsu da ke Aggah Plantation a jihar Rivers da kuma Umudike Plantation, inda aka ɓoye makaman da aka sace da sauran makaman da ake amfani da su wajen aikata laifuka.

    A yayin samamen, an ƙwato bindigogi da alburusai da dama da sauran kayan aikinsu.

    Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike kan waɗanda ake zargin kafin gurfanar da su a gaban kotu, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da yaƙi da masu aikata laifuka domin tabbatar da zaman lafiya a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya.

  9. Saudiyya ta buƙaci Trump kada ya ƙaddamar da harin da ake shiri kan Iran

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya buƙaci Donald Trump da kada ya ƙaddamar da babban harin da ake shiri kai wa Iran, saboda fargabar ƙarin taɓarɓarewar tsaro a yankin, kamar yadda rahoton Axios ya bayyana.

    A cewar rahoton, Bin Salman ya nemi Trump ya rage ƙamari tare da kauce wa kai hare-haren, yayin da Saudiyya kuma ta nemi ƙarin bayani kan shirin ayyukan sojin Amurka.

    Rahoton ya ce Trump na duba yiwuwar kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran a kwanaki masu zuwa, amma har yanzu bai yanke hukunci na ƙarshe ba.

    A lokaci guda, Qatar, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Turkiyya da Pakistan na ƙoƙarin rage rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran.

    An kuma samu wasu ci gaba a tattaunawar da ake yi domin sake buɗe mashigar Hormuz, ko da yake har yanzu ba a tabbatar ko hakan zai hana rikicin ƙara ta'azzara ba.

  10. Ba za mu bari a yi amfani da ƙasarmu wajen kai hari kan maƙwabta ba - Iraq

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Iraq, Mohammed Shia al-Sudani, ya ce gwamnatinsa ba za ta amince a yi amfani da ƙasar ba domin kai hare-hare ko barazana ga ƙasashen maƙwabta.

    A yayin wani taron gaggawa da ya jagoranta domin duba halin tsaro a yankin, Sudani ya ba da umarnin kafa kwamitin tsaro na haɗin gwiwa da kuma samar da matakan hana sake faruwar irin waɗannan ayyuka.

    Ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da bin doka, ƙarfafa zaman lafiya da tsaro, tare da kare ikon mallakar ƙasar da kyakkyawar alaƙa da maƙwabta.

    Sanarwar taron ta ce dakarun Iraq suna cikin shirin ko-ta-kwana don dakile duk wani yunƙuri da za a yi daga cikin ƙasar domin cutar da ƙasashen da Baghdad ta bayyana a matsayin “ƙawayenta da ‘yan’uwanta.

  11. Iran ta ce a shirye take tsaf ta kare muradu da tsaron ƙasarta

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta ce ƙasar a shirye take ta kare muradunta da tsaron ƙasarta bayan sabbin barazanar da Amurka ta yi na kai mata hari.

    A cikin wata sanarwa, Iran ta bayyana hare-haren Amurka a matsayin “haramtattu”, tare da zargin cewa an kai su ne da haɗin gwiwar Isra’ila da wasu ƙasashen yankin.

    Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka da wasu ƙawayenta na yankin suna amfani da batun zirga-zirgar jiragen ruwa a kudancin yankin a matsayin kariya ga ayyukan soja.

    Iran ta jaddada cewa ba ta da wata gaba da ƙasashen yankin Tekun Fasha, tana kuma neman kyakkyawar dangantaka da su.

    Ta kuma ce duk wani martani da take bayarwa zai kasance kan waɗanda suka kai mata hari ne, ba kan ƙasashen yankin ba.

    Sanarwar ta zo ne yayin da ofisoshin jakadancin Amurka a Gabas ta Tsakiya suka gargadi ‘yan ƙasarsu da su kasance cikin shiri saboda yiwuwar ƙarin tashin hankali a yankin.

  12. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiyar ranar Lahadi.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.