Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniy

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 24/05/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ahmad Bawage

  1. Likitoci a Khartoum sun yi gargaɗin ɓarkewar kwalara a ɗaukacin birnin

    Likitoci a Khartoum babban birnin Sudan sun yi gargaɗin ɓarkewar cutar kwalara a birnin baki-ɗaya.

    Ƙarancin wutar lantarki da hare-haren da sojoji ke kai wa ya kawo cikas ga samar da ruwa, kuma mazauna yankin na shan gurɓataccen ruwa.

    Lamarin ya kara kamari cikin gaggawa tun bayan da mayakn RSF suka fara kai hari kan tashoshin lantarki da wuraren adana man fetur makonni uku da suka gabata.

    Ma'aikatar lafiva ta ƙasar ta sanar da mutuwar mutane sama da 50, yayin da cutar ta ƙara bazuwa sakamakon ƙarancin ayyukan jinya a birnin Khartoum.

    Ana ci gaba da gwabza faɗa tsakanin sojojin Sudan da dakarun sa-kai na RSF a yammacin kasar.

    Dubban mutane ne suka rasa matsugunansu a yankunan Darfur da Kordofan.

  2. Harin Isra'ila ya kashe mutum 70 a Gaza, in ji ma'aikatan lafiya

    Masu aikin ceto da na kiwon lafiya a Gaza sun ce sama da mutane 70 ne suka mutu sakamakon hare-haren da Isra'ila ta kai musu ranar Juma'a.

    Asibitin Nasser da ke Khan Younis a kudancin Gaza ya ce wani harin makami mai linzami da Isra'ila ta kai gidan wata daga cikin likitocinsa, ya kashe 'ya'yanta tara, da kuma raunata mijinta.

    Hotunan bidiyo sun nuna gawawwakin kananan yara a ƙone bayan harin.

    Rundunar sojin Isra'ila ba ta ce uffan ba kan rahotannin.

    Tun da farko, Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce mutane a Gaza suna jurewa abin da ka iya zama 'mafi munin yanayi na yaƙin.

  3. Wasu manyan ƴan bindiga ne aka kashe lokacin Tinubu?

    A daidai lokacin da ake fargabar mayar da hannun agogo baya a ƙoƙarin daƙile matsalar tsaro a arewacin Najeriya, wasu na ɗiga alamar tambaya kan me ya sa ake kwan-gaba-kwan-baya a yaƙin.

    A tsakanin watan Maris zuwa watan Afrilu, an fuskanci hare-hare a yankin arewa maso gabashin Najeriya, waɗanda ake zargin tsagin Boko Haram na ISWAP da kaiwa, ciki har da waɗanda suka kai sansanin sojoji.

    Wannan ya sa masana suke ganin lamarin na da ɗaga hankali musamman ganin ƴan ƙungiyar suna amfani da jirage marasa matuƙa, sannan suna amfani da nakiyoyi da suke birnewa a ƙasa.

  4. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barkan mu da safiyar Asabar.

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa.

    Ku kasance da mu domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Ahmad Bawage ne zai kasance da ku a wannan safiya!