An harbe wasu Isra'ilawa biyu a birnin Washington na Amurka
An harbe wasu ma'aikatan ofishin jakadancin Isra'ila biyu, mace da namiji a birnin Washington a lokacin da suke barin wani taro a wani gidan tarihin Yahudawa.
Shugaban ƴansandan birnin Pamela Smith, ta ce wani mutum mai suna Elias Rodriguez ne ya tunkari waɗanda lamarin ya rutsa da su tare da buɗe wuta, kujma tuni suka kama shi.
Wani da abun ya faru a kan idonsa ya ce mutumin ya yi ta ihun neman yancin Falasɗinawa, yana cewa ya yi hakan ne don nuna goyon baya ga mutanen Gaza.
Babbar Lauyar gwamnatin Amurka Pam Bondi, wadda ofishinta ke kusa da wajen, ta ce ta ruga don ta ga me ke faruwa, kuma abun da ta tarar ya munana, kamar yadda ta ce.