Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 09/10/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 09/10/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. An samu dogayen layuka a gidajen mai da ke Mali

    Janar Assimi Goïta

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Janar Assimi Goïta

    An samu dogayen layukan ababen hawa a gidajen man fetur a Bamako babban birnin kasar Mali bayan shafe' wata guda da mayakan kungiyar da ke da alaka da Al ka'ida suka hana shigo da man fetur ta hanyar kai wa manyan motoci masu dakon mai hari a manyan hanyoyin kasar.

    Wasu daga cikin gidajen mai da aka tilastawa rufewa a makon daya gabata a yanzu sun sake budewa bayan tankokin mai fiye da 300 sun shiga cikin kasar daga Ivory tare da rakiyar sojojin.

    Gwamnatin sojin ta ba ‘yan kasar tabbacin cewa lamarin na dan lokaci ne, amma kuma akwai fargabar man da ake ajiye da shi zai iya karewa a dan lokaci kankani, baya ga wasu da ke korafi game da karuwar farashinsa.

    A ‘yan makonnin nan ma akwai birane da wasu sassan kasar da suka yi fama da karancin man da ma wutar lantarki.

    Wasu daga cikin al’ummar kasar musamman a yankin Mopti na ci gaba da korafin yadda kasuwancinsu ke ci gaba da fuskantar matsala musamman wadanda ke safarar danyen kifi domin kuwa karancin wutar lantarkin na barazana ga yadda zaake adana shi.

    Shekaru biyar da suka gabata, lokacin da gwamnatin sojin kasar ta kwace mulki, ta samu gagarumin goyon bayan al’ummar ta Mali, inda ta dauki alkawurra da dama cikin su har da kawo karshen matsalar tsaro da ‘yan aware wadanda galibinsu ‘yan kabilar buzaye ne da kuma ke da karfin iko a arewacin kasar suka haddasa, kuma daga bisani mayakan IS suka goya musu baya.

    Wasu hotunan da aka yada a kafafen sada zumunta, sun nuna yadda jama’a suka yi dandazo a gidajen mai da ke Bamako babban birnin kasar inda suke kwashe tsawon lokaci sun jira.

    Wani gidan rediyo mai suna Nostalgia ya ruwaito cewa farashin mai a birnin na Bamako ya karu da fiye da kashi 200 cikin dari.

    Gwamnatin kasar dai ta bayyana cewa tana yin duk mai yuwa domin samar da mafita.

  2. Amurka da Brazil za su dinke barakar da ke tsakaninsu

    Luiz Inácio Lula da Silva

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Luiz Inácio Lula da Silva

    Da alama danganta tsakanin ƙasashen Amurka da Brazil ta fara daidaita bayan da a karon farko cikin shekara ministocin harkokin wajen ƙasashen biyu suka tattauna ta wayar tarho.

    Tatattaunawar tasu na zuwa ne ƴankwanaki bayan ta Shugaba Trump na Amurka da Luiz Inácio Lula da Silva na Brazil da suka yi suma ta wayar.

    A watan Augustan daya gabata ne Amurka ta sanyawa kayan da ake shigowa da su cikin kasarta daga Brazil harajin kashi 50 cikin 100, da sanyawa alkalan kotun kolin kasar takunkumi kan zargin take 'yancin fadin albarkacin baki, da gallazawa 'yan siyasa 'yan hammaya.

    An sanar da wadannan matakan ne bayan da aka yankewa tsohon shugaban kasar Jair Bolsanaro, hukuncin dauri a gidan kaso kan yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba bayan shan kaye a zabe da aka yi a kasar.

  3. Wane ne Farfesa Joash Amupitan da ke kan hanyar zama sabon shugaban INEC?

    Farfesa AMUPITAN

    Asalin hoton, JABU

    A ranar Alhamis ne Majalisar Magabata a Najeriya ta amince da Farfesa Joash Ojo Amupitan don zama sabon shugaban hukumar zaɓen ƙasar INEC.

    Cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar, ta ce Shugaba Tinubu ne ya gabatar da sunan Farfesa Amupitan ga majalisar domin neman cewarta, inda ita kuma nan take ta amince da shi ba tare da saɓani ba.

    Shugaba Tinubu ya shaida wa Majalisar cewa Farfesa Amupitan ba ɗan siyasa ba ne.

    An haifi Farfesa Amupitan ranar 25 ga watan Afrilun 1967 a garin Ayetoro Gbede da ke yankin ƙaramar hukumar Ijumu a jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya.

    Ya yi karatunsa na furamare da sakandire a Kwara, sannan ya halarci Kwalejin Fasaha da ke Ilorin daga 1982 zuwa 1984, sannan ya zarce jami'ar Jos inda ya karanta fannin shari'a daga 1984 zuwa 1987, inda ya zama lauya a 1988.

    Ya samu digirinsa na biyu a fannin shari'a a jami'ar Jos a shekarar 1993, sannan ya kammala digirinsa na uku a dai jami'ar a 2007.

    Ya fara koyarwa a hukumar wallafa ta jihar Bauchi bayan kammala yi wa ƙasa hidima a shekarun 1988 zuwa 1989.

    A yanzu haka shi ne mataimakin shugaban Jami'ar Jos, kuma shugaban hukumar gudanarwar jami'ar Joseph Ayo Babalola da ke jihar Osun.

    A yanzu haka Farfesa ne a fannin shari'a a Jami'ar Jos da ke jihar Filatom.

    A shekarar 2014 ne ya samu babban muƙamin lauyoyi na SAN

  4. Mata ma'aikata za su fara hutu idan suna jinin al'ada a India

    Audugar mata

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Audugar mata

    Hukumomi a jihar Karnataka da ke Kudancin Indiya sun amince da bai wa mata ma'aikatan gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu hutun kwana guda a kowanne wata idan su na jinin al'ada.

    Karamin ministan cikin gida Siddaramaiah, ya kira matakin da na jin kai, da fahimtar halin da mata ke ciki da samar musu da walwala a wurin aiki.

    Jihar Karnataka, ita ce cibiyar ma'aikatar fasaha ta Bengaluru da ta fi kowacce jiha daukar mata ma'aikata a India.

    A hukumance Ita ce jiha ta farko da ta sanar da bai wa matan da ke aiki a ma'aikatun gwamnati da masu zaman kansu a hutu lokacin jinin al'ada a daukacin kasar.

    Jihohi kamar Bihar da Kerala ba su da cikakkun tsari kan hakan.

  5. An hana hukunta ministocin Italiya da suka sa aka saki Osama Almasri Najim

    Osama Almasri Najim

    Asalin hoton, @MarcoFattorini / X

    Bayanan hoto, Osama Almasri Najim

    'Yan majalisar Italiya sun hana yunkurin hukunta ministocin gwamnati biyu kan sakin wani jami'in Libya da ake zargi da aikata laifukan yaki.

    Tun a watan Janairun bana ake tsare da Osama Almasri Najim, tsohon dansandan hukumar shari'ar Libya, bayan kotun ICC ta bada sammacin kama shi.

    Daga bisani an sake shi tare da mayar da shi birnin Tripoli ta amfani da jirgin sojin sama na Italiya, inda ministan shari'ar kasar Carlo Nordio,ya ce sammacin kama shi na cike da kura-kurai.

    A yanzu 'yan majalisar kasar ta masu ra'ayin sauyi mai rinjaye ta kada kuri'ar kin amincewa da hukunta Mr Nordio da ministan cikin gida Matteo Piantedosi.

    Ana zargin Mr Najim da laifin aikata kisa da fyade da azabtarwa a lokacin da ya ke shugabantar gidan kason Mitiga da ke birnin Tripoli na Libya.

  6. An yi arangama tsakanin 'yansanda da masu zanga-zanga a Madagascar

    'Yansanda sun kama mai zanga-zanga

    Asalin hoton, LUIS TATO/AFP

    Bayanan hoto, 'Yansanda sun kama mai zanga-zanga

    Dandazon mutane sun yi taho mu gama da 'yan sanda a birnin Antananarivo na kasar Madagascar, a dai-dai lokacin da zanga-zangar kin jinin gwamnatin shugaba Andry Rajoelina ta kara munana.

    Masu zanga-zangar sun toshe hanyoyi da manyan duwatsu, bayan kiran zanga-zangar gama gari da bukatar shugaban kasar ya sauka daga mukaminsa.

    'Yansanda sun mayar da martani da rufe manyan hanyoyin shiga birnin, da kuma cafke masu zanga-zangar da dama.

    Matasan da suka kira zanga-zangar sun yi watsi da kiran shugaba Rajoelina na hawa teburin sulhu, bayan ya rusa majalisar gwamnatinsa da nada wani janar din soji a matsayin firai minista.

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutum 25 aka kashe a boren da ya faro daga rashin ruwa da wutar lantariki, lamarin da ya fusata 'yan kasar.

  7. RSF ta rufe birnin El-Fasher yayin da hare-hare ke ƙara ƙamari a Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun RSF sun kammala gina gatanta mai tsawon kilomita 57 da ta kewaye birnin El Fasher, wanda hakan ya rufe duka hanyoyin fita daga birnin tare da ƙulle dubban fararen hula a ciki, kamar yadda rahoton Jami’ar Yale ya nuna.

    Hotunan tauraron dan adam sun tabbatar da cewa RSF ta ƙarfafa shinge a ƙofar Mellit, ɗaya daga cikin hanyoyin fita huɗu na birnin.

    Rahoton ya bayyana wannan mataki a matsayin sabon mataki na tashin hankali da kisan gilla a yankin.

    An gano gidaje da dama da aka ƙone a unguwar Daraja Oula tsakanin 4 zuwa 8 ga Oktoba wanda ake kyautata zaton RSF ne ta aikata hakan.

    Rahoton ya kuma ce mutanen da ke ƙoƙarin tserewa suna fuskantar tsarewa da batar da su da kuma fyade.

    Masana a Jami’ar Yale sun yi gargaɗin cewa irin waɗannan hare-hare na iya ƙaruwa yayin da RSF ke ƙoƙarin karɓar cikakken ikon El Fasher, inda ake fama da yunwa da matsanancin hali.

  8. Majalisa Magabata a Najeriya ta amince da nadin sabon shugaban INEC

    Farfesa

    Asalin hoton, JABU

    Majalisar magabata a Najeriya ta amince da nada Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN) daga jihar Kogi da ke tsakiyar kasar a matsayin sabon shugaban hukumar zaben kasar.

    Cikin wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar, ta ce Shugaba Tinubu ne ya gabatar da sunan Farfesa Amupitan ga majalisar domin neman amincewarta.

    Matakin na zuwa ne kwana uku bayan murabus din tsohon shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu, wanda wa'adinsa ya kare.

    Tinubu ya shaida wa majalisar cewa Farfesa Amupitan ne mutum na farko daga jihar Kogi da zai rike mukamin, kuma ba dan siyasa ba ne.

    Nan take kuma duka mambobin majalisar suka amince da shi ba tare da sabani ba.

    A yanzu shugaba Tinubu zai aika sunansa zuwa majalisar dattawan kasar domin amincewarta kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

    Farfesa Amupitan, mai shekara 58, malami ne a Jami'ar Jos da ke jihar Plateau.

    A 2014 ne ya samu mukamin babban lauya na SAN.

  9. Faransa za ta shirya taro kan makomar Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Faransa za ta gudanar da wani taro a birnin Paris ranar Alhamis tare da ƙasashen Larabawa da Turai don tattauna shirin makomar Gaza idan aka cimma tsagaita wuta.

    Ministoci daga Masar da Jordan da Saudiyya da Qatar da UAE za su halarci taron, tare da wakilai daga Birtaniya da Italiya da Jamus da Spain da Turkiyya da Tarayyar Turai amma babu Isra’ila a ciki.

    Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta ce: “Wannan taro zai ba da damar aiwatar da shirin zaman lafiya da tsara tsarin makomar Gaza ta hanyar fayyace abubuwan da aka amince da su."

    Ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce taron an shirya shi ne ba tare da sanin Isra’ila ba.

    Zaman ɗarɗar tsakanin Isra’ila da wasu ƙasashe ya ƙaru, ciki har da Faransa tun bayan fara yaƙin.

  10. Yadda Falasɗinawa ke murna bayan jin labarin yarjejeniyar tsagaita wuta

    Kamar yadda muka ruwaito a baya shugaban Amurka, Donald Trump ya sanar da cewa Hamsa da Isra'ila sun cimma matsaya kan matakin farko na shirin samar da zaman lafiya a Gaza bayan doguwar tattaunawa a Masar,

    Duk da cewa yarjejeniyar ba ta fara aiki ba tukuna, kuma har yanzu ana tattaunawa kan muhimman bayanai na yarjejeniyar, an ga Falasɗinawa sun fito kan titunan Gaza suna murnar labarin.

    ...

    Asalin hoton, EPA

    ...

    Asalin hoton, EPA

    ...

    Asalin hoton, EPA

    ...

    Asalin hoton, EPA

  11. Ana sa ran gwamnatocin Isra’ila za su amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa Isra'ila da Hamas sun cimma matsaya kan matakin farko na tsagaita wuta a Gaza, ana sa ran yarjejeniyar za ta fara aiki ne kawai idan gwamnatocin Isra’ila sun amince da ita.

    Ana sa ran majalisar tsaron Isra’ila za ta gana yau da karfe 5 ta yamma don tattauna yarjejeniyar, kafin a tura ta zuwa ga majalisar domin kaɗa ƙuri’a.

    A cikin Isra’ila, ana ganin kusan tabbacin cewa za a amince da yarjejeniyar.

    Firaminista Benjamin Netanyahu ya bayyana yarjejeniyar a matsayin "babbar nasara a garasu".

  12. Majalisar wakilai ta yi watsi da zargin kisan Kiristoci a Najeriya

    ...

    Asalin hoton, NATIONAL ASSEMBLY

    Majalisar Wakilai ta ƙi amincewa da iƙirarin da Amurka ta yi na cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya saboda addini, tana mai cewa wannan labari ba gaskiya ba ne kuma yana da ruɗani.

    Majalisar ta kuma buƙaci a samu haɗin kai tsakanin diflomasiyya da hukumomin cikin gida wajen mayar da martani kan ƙudirin doka da ake shirin gabatarwa a Majalisar Dattawan Amurka, wanda ke neman a saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da ke take hakkin ‘yancin addini.

    Wannan mataki ya biyo bayan ƙudirin da mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Okezie Kalu, da wasu ‘yan majalisa suka gabatar a zaman majalisar na ranar Laraba.

    A kwanakin baya, ɗan majalisar Amurka, Sanata Ted Cruz, ya gabatar da ƙudiri domin kare Kiristoci a Najeriya daga abin da ya bayyana a matsayin cin zarafi da kisa saboda addini.

  13. Hukumar PCACC na binciken Ganduje kan zargin karkatar da kuɗaɗe

    ...

    Asalin hoton, Salihu Tanko

    Hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar Kano a Najeriya wato PCACC, ta ce ta fara gudanar da cikakken bincike kan zargin karkatar da wasu kudade fiye da naira bilyan hudu da tsohuwar gwamnatin jihar Dr Abdullahi Umar Ganduje ta yi.

    Shugaban hukumar, Saidu Yahaya ya ce binciken da hukumar tasu ta fara gudanarwa ya biyo bayan wani ƙorafi ne da aka kai musu game da batun kuɗaɗen na naira sama da biliyan huɗu da ake zargin tsohuwar gwamnatin Ganduje ta karkatar

    "A taƙaice, muna gudanar da bincike a kan wasu kuɗaɗe da aka ɗauka daga gwamnatin jahar Kano aka je aka saka a cikin Dala Inland Dry Port." in ji shi

    "Wannan kudin ya kai sama da naira biliyan huɗu, kuma an ɗauke su ne a lokacin mulkin Abdullahi Ganduje.

    Yayin da BBC ta nemi jin ta bakin malam Muhammad Garba, tsohon kwamishinan yaɗa labarai na jahar kuma tashon shugaban ma'aikatan tsohon gwamnan Dr Abdullahi Ganduje game da wannan bincike da aka fara, sai ya ce

    "Nasan cewa maganar tana kotu to kuma idan magana tana kotu, ban san irin binciken da za ayi ba,."

    "Da na tuntuɓi mai girma tsohon gwamna, Ganduje,wannan binciken ba wani abu ba ne na damuwa, dama ai an saba ana gudanar da irin wannan bincike a wurare daban-daban." In ji Muhammad Garba.

  14. Fadar shugaban ƙasa ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan Talauci

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar shugaban ƙasa ta maida martani kan rahoton Bankin Duniya da ya ce mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a Najeriya, inda ta ce ƙididdigar ba ta nuna hakikanin halin da ake ciki a ƙasar ba.

    A cewar fadar shugaban ƙasa, Bankin Duniya ya yi amfani da ƙa’idar duniya wadda ke ɗaukar duk wanda ba ya samun sama da dala $2.15 a rana a matsayin talaka.

    Wannan ƙa’ida an kafa ta ne tun shekarar 2017, kuma idan aka fassara ta zuwa kuɗin Najeriya a yau, ta kai kusan Naira 100,000 a wata fiye da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 kenan.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Fadar shugaban ƙasa ta fitar wanda Sunday Dare, mai magana da yawun shugaban ƙasa ya fitar a shafinsa na X.

    'Bayanan da Bankin Duniya ya dogara da su tsofaffi ne tun daga shekarar 2018/2019, kuma ba su haɗa da tattalin arzikin yanzu ba. Saboda haka, gwamnati ta bayyana cewa wannan adadi misali ne na ƙididdigar duniya, ba ainihin yanayin da ake ciki a shekarar 2025 ba."

    A cewar fadar shugaban ƙasa, abin da ya fi muhimmanci shi ne hanyar da ake bi wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa, amma kuma Bankin Duniya ta ce sauye-sauyen Tinubu ba su rage talauci ba.

    Ta ce "gwamnatin Shugaba Tinubu tana mai da hankali ne wajen rage wahalar tattalin arziki ta hanyar shirye-shirye na musamman kamar tallafin kuɗi ga talakawa, da bashin karatu na ɗalibai, da sauransu."

  15. Cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza babbar nasara ce garemu - Netanyahu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya kira yarjejeniyar tsagaida wuta a Gaza da aka cimma a matsayin babbar nasara ga Isra'ila yana mai cewa zai kira taron majalisar zartarwa a yau Alhamis domin amincewa da ita.

    Ya zanta da shugaban Amurka, Donald Trump ta wayar tarko inda ya gode masa kan jagorancinsa tare da gayyatarsa domin yin jawabi a gaban majalisar Isra'ila.

    Ƙungiyar Hamas ta yi maraba da yarjejeniyar tana mai cewa ta tanadi tsarin kawo karshen yaƙin.

    Hamas ta kuma buƙaci Trump ya tabbatar da Isra'ila ta mutunta sharuɗɗan yarjejeniyar.

    Duk da fatan yarjejeniyar za ta kawo ƙarshen yaƙin, akwai muhimman batutuwan da dole a tattauna da suka haɗa da wanda zai jagoranci Gaza da kuma makomar Hamas.

    An yi ta murna a Gaza bayan sanar da labarin amincewa da yarjejeniyar.

  16. Abu biyar da za a dinga tuna tsohon shugaban INEC Mahmood Yakubu da su

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayan shekara 10 yana jagorantar hukumar zaɓen Najeriya mai zaman kanta, a ranar Talata ne Farfesa Mahmood Yakubu ya ajiye aiki a hukumance bayan kammala wa'adi biyu na jagorancin hukumar.

    Nan take kuma Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci May Agbamuche-Mbu ya maye gurbinsa a matsayin shugaban riƙo na hukumar ta Independent National Electoral Commission (INEC).

    A ranar 21 ga watan Oktoban 2015 Tsohon Shugaban Ƙasar Marigayi Muhammadu Buhari ya naɗa Yakubu a matsayin shugaban INEC.

    Shi ne ya jagoranci gudanar da manyan zaɓukan ƙasa biyu; na 2019 da 2023, da kuma zaɓukan cike gurbi masu yawa.

  17. Mutum miliyan 139 na cikin ƙangin talauci a Najeriya - Bankin Duniya

    ...

    Asalin hoton, Facebook/Bola Tinubu

    Babban Bankin Duniya ya ce har yanzu Najeriya na cikin ƙangin talauci duk da cewa an samu bunƙasa a tattalin arziƙin ƙasar da ƙaruwa a samun kuɗaɗen shiga inda Babban Bankin ya ce gyare-gyaren Tinubu ba su rage talauci ba.

    Babban Bankin ya bayyana cewa sama da mutane miliyan 139 a Najeriya na rayuwa cikin talauci a shekarar 2025, duk da matakan gyaran tattalin arziƙi da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauka.

    Daraktan ƙasa na Babban Bankin Duniya a Najeriya, Mathew Verghis, ne ya bayyana haka a Abuja yayin ƙaddamar da rahoton cigaba Nigeria inda bankin ya kuma yi hasashen cewa tattalin arziƙin Najeriya zai bunƙasa da kashi 4.4 cikin 100 a shekarar 2027.

    Wannan na zuwa ne bayan makonni kaɗan da Tinubu ya yaba wa gwamnatinsa bisa abin da ya kira “sake farfaɗowar tattalin arziƙin ƙasa.

    Tinubu ya faɗi hakan ne a yayin jawabinsa na ranar murnar cika shekaru 65 da samun ’yancin kai inda ya ce gyare-gyaren tattalin arziƙi da zamantakewa da gwamnatinsa ta aiwatar sun fara ba da sakamako.

  18. Isra’ila da Hamas sun cimma yarjejeniyar matakin farko ta zaman lafiya a Gaza

    ...

    Bayan doguwar tattaunawa a Masar, Isra'ila da Hamas sun cimma matsaya kan matakin farko na shirin samar da zaman lafiya a Gaza.

    Matakin ya ƙara girman fatan da ake da shi na kawo ƙarshen yaƙin shekaru biyu.

    Shugaban Amurka, Donald Trump ne ya sanar da matakin wanda ya kira babbar rana ga duniya kuma matakin farko na tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

    Yarjejeniyar ta ƙunshi tsagaita buɗa wuta, da kuma sakin dukkanin yan Isra'ila da Hamas ke garkuwa da su, yayin da kuma Isra'ila za ta saki Falasɗinawa da take tsare da su da kuma janye dakarunta daga Gaza.

    Shugaba Trump kenan ke shaida wa kafar yada labarai ta Fox cewa a ranar Litinin ne za a saki mutanen da aka yi garkuwa da su

  19. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a yau Alhamis.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kuma kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.