Isra'ila ta tsananta hare-hare a Gaza
Sojojin Isra'ila sun tsananta kai hare-hare a arewacin Gaza, inda cikin dare, aka samu rahoton mutuwar sama da mutane hamsin.
Likitoci sun ce yara na daga cikin wadanda aka kashe a hare haren da aka kai a sansanin ƴan gudun hijira na Jabalia.
An kai hare-haren ne ta sama, bayan da Isra'ila ta ba da umarnin ficewa, tare da gargadin fararen hula da su kara nausawa kudancin kasar.
Ko a jiya Talata, sai da wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani katafaren asibiti a Khan Younis da ke kudancin zirin, ya yi sanadin asarar rayuka da dama.
Rahotanni sun ce Isra'ilar na fakon dan uwan shugaban Hamas da aka kashe Yahya Sinwar ne.