KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 22/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwaftan ƙasashe da kuma sauran sassan duniya na ranar Asabar 21 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Tinubu ya taya ‘yar Gombe murnar lasha gasar musabaka ta duniya

    Maryam

    Asalin hoton, Bayo Onanuga

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Maryam Ibrahim Dan’Azumi, ‘yar asalin Jihar Gombe murnar lashe gasar musabakar Alqur'ani bangaren mata ta duniya ta King Abdulaziz International Qur’anic Competition da aka gudanar a kasar Saudiyya.

    Maryam ta zama ta farko a rukunin mata a gasar da aka gudanar a birnin Makkah, inda ta doke sauran mahalarta daga ƙasashe 132 na duniya.

    Maryam ta samu riyalan Saudiyya 300,000, wanda ya yi daidai da kusan naira miliyan 120 a matsayin kyauta.

    Shugaba Tinubu ya yaba wa Maryam bisa ƙwarewa da bajintar da ta nuna wajen haddacewa, karatu da fahimtar Alƙur’ani mai girma. Ya ce nasarar ba ta Maryam kaɗai ba ce, inda ya ce ta zama abin alfahari ga Najeriya baki ɗaya, domin ta ɗaga darajar ƙasar a fagen duniya.

    Tinubu ya kuma bayyana Maryam da ‘yar’uwarta, Hajara Ibrahim Dan'Azumi, a matsayin abin koyi ga matasan Najeriya.

    Hajara ita ma ta samu nasara a wata makamanciyar gasar Alƙur’ani da aka gudanar a Jordan a shekarar 2024, inda ta zo ta farko.

    Shugaban Ƙasar ya yaba wa iyayensu, malamansu da masu kula da tarbiyyarsu, yana mai cewa irin wannan matsayi na ƙwarewa yana buƙatar sadaukarwa, jajircewa da kyakkyawar tarbiyya.

    A ƙarshe, Tinubu ya yi wa Maryam addu’ar Allah Ya ƙara mata ilimi da hikima, Ya kuma ba ta damar ci gaba da samun nasara a karatun Alƙur’ani da sauran abubuwan da za ta gudanar a rayuwarta.

  2. An yi amfani da mutum-mutum wajen tiyata a Najeriya

    Hope Uzodimma Facebook page

    Asalin hoton, Hope Uzodimma Facebook page

    Jihar Imo ta samu gagarumar nasara a fannin kiwon lafiya, bayan kammala tiyatar da aka yi da taimakon na’urar mutum-mutumi a karon farko a asibitin Specialist Hospital da ke Umuguma, Owerri.

    Tawagar ƙwararrun likitoci ‘yan Najeriya da na ƙasashen waje ce ta gudanar da tiyatar, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Kingsley Ekwueme, wani ƙwararren likitan tiyatar mutum-mutumi da ke aiki a Birtaniya, amma ɗan asalin Jihar Imo.

    Da yake magana da manema labarai a cibiyar Imo Robotics and Oncology Centre (IROC), inda aka gudanar da tiyatar, Farfesa Ekwueme ya bayyana aikin da “cikakkiyar nasara," kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

    Ya jaddada cewa wannan fasaha na da matuƙar amfani wajen maganin ciwon daji na kasan mafitsara, domin a cewarsa tana bai wa likitoci damar cire ƙwayoyin da ke ɗauke da ciwon daji tare da kare muhimman ayyukan jiki, ciki har da ikon yin fitsari da karfin jima’i.

    Ekwueme ya ce nasarar tiyatar mutum-mutumi wajen maganin ciwon daji, musamman na kasan mafitsara, tana da matuƙar girma, kuma marasa lafiya bai kamata su sha fama da rashin iya riƙe fitsari ko rasa karfin jima’i na dogon lokaci bayan tiyatar ba.

    Gwamna Hope Uzodimma, wanda ya shaida wannan gagarumar nasara, ya ce hakan babban mataki ne wajen samar da ingantaccen kiwon lafiya mai araha ga al’ummar jihar.

    Ya ce cibiyar ba za ta kasance wurin kula da marasa lafiya kawai ba, har ma za ta taimaka wajen gano cututtuka tun da wuri da kuma rigakafinsu ta hanyar duba lafiyar jama’a akai-akai.

    Uzodimma ya bayyana cewa cibiyar tana aiki ne ƙarƙashin tsarin haɗin gwiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu (PPP), inda mafi yawan kuɗaɗen gudanar da ita ke fitowa daga ɓangaren masu zaman kansu. A cewarsa, hakan zai taimaka wajen tabbatar da dorewar cibiyar da ingantaccen gudanar da ita.won lafiya na musamman.

  3. ICPC ta sake bankado wata hukumar bogi a Najeriya

    Tinubu

    Asalin hoton, @icpcnigeria/X

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan wata sabuwar hukumar gwamnati da ake zargin ta bogi ce, wadda hukumar yaƙi da cin hanci ta ƙasar ta gano.

    Wannan lamari ya biyo bayan wani makamancin bincike da ya shafi wata hukuma da gwamnati ta ce an gabatar da ita a matsayin hukumar gwamnati, alhali ba haka ba ne.

    Hukumar ICPC ta ce hukumar ta National Brands Development and Made in Nigeria Special Project Office tana gudanar da ayyukanta ba bisa ƙa’ida ba daga wani ofishin gwamnati da ke Abuja.

    Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu, ya ce an ware wa hukumar wannan ofishin ne a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, ba tare da amincewar Shugaban Ƙasa ba.

    Ya bayyana cewa an gano hakan ne yayin wani babban bincike da Shugaba Tinubu ya bayar da umarni a gudanar, bayan wani rahoto na baya da ya shafi Presidential Foreign Intervention Promotion Council, wadda ake zargin ƙungiya ce da ba ta wanzu a zahiri.

    A cewar Aliyu, wani mutum mai suna George Buchi Nwabueze ne ya ke tallata sabuwar hukumar, kuma ana zargin yana amfani da sunaye daban-daban.

    ICPC ta ce tana binciken yadda aka ba wannan ofishi damar gudanar da ayyukansa daga harabar gwamnati, da kuma ko wasu jami’an gwamnati sun taimaka wajen ba shi damar yin hakan.

    Har yanzu ba a bayyana ko Nwabueze ya samu kuɗi daga wannan zargin ba kafin a gano lamarin.

    A cewar ICPC, Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin a kama Nwabueze ba tare da bata lokaci ba.

    Shugaban ƙasar ya kuma bayar da umarnin dakatar da wasu manyan jami’an gwamnati da ake zargi suna da alaka da hukumar, in ji Aliyu.

    A baya dai wani bincike daban da aka gudanar kan Presidential Foreign Intervention Promotion Council, wadda fadar shugaban ƙasa ta ce ba ta bogi ce.an hukumomin da ake zargin na bogi ne.

  4. Sakataren sojin kasan Amurka zai yi murabus

    Amurka

    Asalin hoton, Reuters

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito daga Mujallar Wall Street cewa ana sa ran Sakataren Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka, Dan Driscoll, zai yi murabus kafin ƙarshen shekara, bayan watanni ana samun takun-saka tsakaninsa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth.

    Mujallar Wall Street Journal ta wallafa rahoton ne bisa bayanan wasu mutane da ke da masaniya kan dambarwar.

    Sai dai Reuters ta ce har yanzu ba ta samu damar tabbatar da rahoton da kanta ba.

    Idan aka tabbatar da murabus ɗin Driscoll, hakan zai sa Rundunar Sojin Ƙasa ta Amurka ta kasance ba tare da shugaba da Majalisar Dattijan Amurka ta tabbatar da nadinsa ba, a daidai lokacin da Washington ke ci gaba da yaƙi da ta ƙaddamar tare da Isra’ila kan Iran, wanda yanzu ya shafe kusan wata shida.

  5. APC ta nada Abdulaziz Yari Darakta-Janar na yakin zaben Tinubu

    Yari

    Jam’iyyar APC ta kafa Kwamitin yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa, inda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, ya kasance Darakta Janar (DG) na kwamitin.

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima za su kasance shugaba da mataimakin shugaban kwamitin, sannan Gwamna Hope Uzodimma kuma zai yi aiki a matsayin sakataren kwamitin.

    A cikin tsarin kwamitin, an haɗa manyan jami’an jam’iyyar da gwamnati domin jagorantar shirye-shiryen yaƙin neman zaɓen da ake tunkarar zaɓen Janairu 2027.

    Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin da su yi aiki tukuru domin ganin APC ta samu nasara a zaɓen.

  6. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Asabar a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.