Yadda ƴansanda suka yi amai suka lashe kan sace mutane a Kaduna
Rundunar ƴansandan Najeriya ta sanar da sauya matsayar da ta ɗauka a baya cewa ba a sace mutane ba a garin Kurmin Wali na ƙaramar hukumar Kajuru ta jihar Kaduna, inda a yanzu rundunar ta tabbatar da garkuwa da mutanen.
A ranar Litinin aka fara samun rahotannin cewa wasu mahara sun shiga ƙauyen na Kurmin Wali tare da sace mutane kimanin 170 a yankin mai fama da matsalar tsaro.
Amma a ranar Litinin ɗin, sarkin Kurmin Wali, Ishaku Dan'azumi ya tabbatar wa BBC cewa maharan sun je ƙauyen ne a ranar Lahadi, inda suka sace mutane sama da 160.
"Sun zo ranar Lahadi wurin karfe 9, lokacin muna coci, suka bazu a garin, suka sa mu a tsakiya.
"Waɗanda suke a hannunsu yanzu 166," in ji Ɗan'azumi.
Shi ma shugaban ƙungiyar CAN a arewacin Najeriya Jospeh Hayab ya tabbatar wa kafafen yaɗa labarai batun sace mutunan a ranar ta Litinin.