Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/06/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Usman Minjibir, Aisha Bbabangida da Annur Muhammad

  1. Ƴansanda sun mamaye hedikwatar jam’iyyar PDP gabanin taronta a Abuja

    Ƴan sanda ɗauke da makamai sun mamaye Wadata Plaza, hedikwatar jam’iyyar PDP da ke Abuja, yayin da tashin hankali ke ƙara ƙaruwa dangane da taron kwamitin zartaswa na Kasa (NEC) da ake sa ran gudanarwa a ranar Litinin.

    Rahotanni sun bayyana cewa 'yan sanda sun hana Maina Chiroma, ɗaya daga cikin mambobin Kwamitin Amintattu na Jam’iyyar, shiga cikin harabar hedikwatar.

    Wani jami’in jam’iyyar, wanda ya yi magana da gidan talabijin na Channels ba tare da bayyana sunansa ba, ya ce an turo 'yan sandan ne domin hana gudanar da taron na NEC da aka shirya.

    Duk da cewa an bar wasu ma’aikatan jam’iyyar sun shiga cikin harabar da farko ba tare da wani cikas ba, daga bisani sai aka tilasta musu fita daga ciki.

    Haka kuma, 'yan jarida da ke wajen sun samu umarnin barin harabar hedikwatar jam’iyyar.

    An hango wasu daga cikin ‘yan sanda suna toshe titin Dalaba Street, wanda ke kai wa kai tsaye zuwa Wadata Plaza.

    Rahotanni dai na cewa a yanzu haka ɓangarori biyu na jam'iyyar na son gudanar da taronsu daban-daban, inda kowane ɓangare ke iƙrarin kasancewa halastacce.

  2. Kanada ta dakatar da harajin fasahar zamani bayan barazanar Amurka

    Gwamnatin ƙasar Kanada ta sanar da dakatar da harajin harkokin fasahar zamani, yan sa'o'i kafin ya fara aiki

    A ranar Juma'a ne dai shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar kawo ƙarshen tattaunawar kasuwanci da Ottawa tare da ƙaƙabawa kanada sabbin haraje-haraje sakamakon tsarin harajin.

    Hukumomin kuɗi na Kanada sun ce za a dakatar da harajin yayin da ake sa ran samun cikakken yarjejeniyar kasuwanci da Amurka.

    Harajin fasahar zai shafi kamfanonin fasaha na Amurka, da suka haɗa da Amazon da Meta da kuma Apple.

    Shugaba Trump ya yi iƙirarin cewa sabon harajin zai iya sake jefa kasuwancin Amurka da Kanada cikin ruɗani bayan a kwashe watanni cikin kwanciyar hankali.

  3. Badaru ya jagoranci tawagar gwamnatin Najeriya domin jana'izar Aminu Dantata

    Wata tawaga daga gwamnatin Najeriya ta isa ƙasar Saudiyya domin jana'izar marigayi, fitaccen ɗan kasuwa kuma dattijo, Alhaji Aminu Alhassan Dantata a birnin Madina.

    Marigayi Dantata ya rasu ne a Abu Dhabi, babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa, a ranar Asabar yana da shekara 94.

    Tawagar ta bar Najeriya da yammacin Lahadi, inda ta isa Madina da safiyar Litinin.

    Tawagar na ƙarƙashin jagorancin ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.

    Sauran mambobin tawagar sun haɗa da ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi (SAN) da ministan yaɗa labarai, Alhaji Mohammed Idris, da ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Hon. Yusuf Abdullahi Ata da dai sauran su.

    Akwai kuma manyan malamai a cikin tawagar da suka haɗa da sheikh Aminu Daurawa da Dr Bashir Aliyu Umar da kuma Khalifa Abdullahi Muhammad.

  4. Gwamnan Kano ya jagoranci wata babbar tawaga zuwa jana’izar Aminu Dantata a Madina

    Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci wata babbar tawaga zuwa birnin Madina na Masarautar Saudiyya domin halartar jana’izar fitaccen ɗan kasuwa kuma dattijo, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata.

    Gwamnan ya tashi daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da daren Litinin, inda ya bayyana girmamawa da mutunta rayuwar marigayin a matsayin wani babban uba ga al’umma.

    A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamna Abba Yusuf yana tare da Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II da gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, da tsohon gwamnan Jigawa, Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sauran manyan jami’an gwamnati da dattawan jihar Kano.

    Marigayi Aminu Dantata, wanda ya shahara wajen kasuwanci da sadaka da hidimar jama’a, ya rasu ne a Abu Dhabi, babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa.

    "Mutuwarsa ta bar giɓi a harkokin tattalin arziki da walwalar al’umma, tare da kammala wani babi mai muhimmanci a tarihin Najeriya." in ji sanarwar.

    Gwamnan yayin da yake zantawa da manema labarai kafin tafiyar, ya bayyana cewa marigayin yana da kyakkyawan tarihi na karamci da kishin jama’a wanda ya zarce ƙasashe da iyakoki.

    "Halartar tawagar Kano a jana’izar alama ce ta matuƙar girmamawa da godiyar da al’ummar Kano ke da ita ga irin gudummawar da marigayin ya bayar a rayuwarsa." sanarwar ta ƙara da cewa

  5. An kashe jami'ai biyu a hari kan masu kashe gobarar daji a Idaho na Amurka

    Jami'an kashe gobara a jihar Idaho na Amurka sun fuskanci hari yayin da suke fafatawa da wata wutar daji a gefen wasu tsaunuka.

    Babban jami'in yansanda na gundumar Kootenai, Bob Norris ya faɗawa wani taron manema labarai cewa an buɗewa ma'aikatan wuta ne da manyan bindigogi wannda hakan yayi sanadin muuwar jami'ai biyu.

    Ya ce ba a san yawan maharan ba, kuma ya zuwa yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba.

    An kwashe sa'o'i da dama ana musayar wuta kuma jami'ai sun bayyana cewa wani dan bindiga ya yi kwanton Ɓauna yayin da ya ke buɗewa jam'ian kashe gobarar wuta.

    'Yan sanda sun ce an gano gawar wani mutum daya, an kuma tsinci bindiga a kusa da ita.

  6. Macron ya buƙaci Iran ta koma kan teburin tattaunawa

    Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na Iran Masoud Pezeshkian.

    Macron ya ce ya kamata Iran ta mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakaninta da Isra'ila, ta kuma koma a ci gaba da tattaunawa kan shirinta na nukiliya da makamai masu linzami.

    Macron ya kuma shaida wa shugaba ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian cewa, ya kamata ƙasarsa ta kiyaye yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliya tare da dawo da haɗin gwiwa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta Majalisar dinkin duniya wato IAEA.

    Ya zuwa yanzu dai Iran ta ƙi amincewa ta bai wa hukumar izinin ta duba cibyoyin nukiliyarta da Amurka da Isra'ila suka jefa wa bama-bamai.

  7. Iran ta ce tana da hakkin ci gaba da aikin nukiliyarta

    Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da inganta sinadarin Uranium, mako guda bayan da Amurka ta haɗa hannu da Isra'ila wajen kai harin bama-bamai a manyan cibiyoyin nukiliyarta.

    Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar Majid Takht-Ravanchi ya shaida wa BBC cewa za a iya tattauna iya matakin da za a iya kai wa na sarrafa sinadarin.

    Ya ce "muna tsakiyar tattaunawa sai kwatsam aka afka mana da hare-hare kuma duk waɗanda ke sukar mu ya kamata su soki irin halin rashin mutuncin da aka nuna mana."

    Mataimakin ministan ya shaida wa wakiliyar BBC da ke ziyara a Tehran cewa gwamnatin ƙasarsa ba za ta shiga wata tattaunawa kan nukiliya ba, sai idan gwamnatin Trump ta ba da tabbacin ba za ta kai mata hari ba yayin da tattaunawar ke gudana.

  8. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a hantsin Litinin.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassa na duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.