Iran da Isra’ila sun yi wa juna ruwan wuta da makamai masu linzami
Iran da Isra’ila sun ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami cikin dare har zuwa safiyar yau Litinin.
Wannan na zuwa ne bayan harin da Iran ta kai arewacin Isra’ila a ranar Lahadi, wanda shi ne na farko tun bayan tsagaita wuta da aka cimma a watan Afrilu.
Tehran ta ce harin da ta kai shi ne na farko, a jerin hare-haren da za ta shafe mako guda tana kai wa Isra'ila, wadda ta zarga da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma ta hanyar kai hari Lebanon.
Zuwa yanzu ba a bayar da rahoton samun asarar rayuka sakamakon hare-haren ba.
Isra'ila ta mayar da martani duk da cewa Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bukaci kada ta ta tanka Iran, saboda hakan na iya mayar da hannun agogo baya.
Yanzu haka rahotanni na cewa dakarun tsaron Isra'ilar sun bada wata sabuwar sanarwar gargadi ga jama'a da ke cewa Iran din ta sake harbo karin wasu makamai masu linzami, don haka jama'a su yi maza su shige wuraren neman mafaka da aka tanada.
Bayanai na cewa ita ma kungiyar Huthi da ke Yemen da Iran din ke mara wa baya ta harba wa kasar makami mai linzami wanda yanzu haka ke kan hanya.