Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Umar Mikail

  1. Ba zan taɓa shiga jam'iyyar PDP ba - El-Rufa'i

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i

    Asalin hoton, fb/Nasir El-Rufa'i

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya bayyana cewa duk da cewa jam'iyyarsa ta APC ta "bar manufofinta na asali" amma ba zai taɓa komawa babbar jam'iyyar adawa ta ƙasar, wato PDP ba.

    El-Rufa'i ya bayyana haka ne a tattaunawar da ya yi da kafar talabijin ta Arise, a yau Litinin.

    Tsohon gwamnan na jihar Kaduna, wanda sanannen ɗan siyasa ne a Najeriya, an riƙa raɗe-raɗi game da makomar siyasarsa bayan sukar da ya riƙa yi wa jam'iyyar APC mai mulki.

    A lokacin tattaunawar, El-Rufa'i ya nanata sukar da yake yi wa jam'iyyar ta APC, inda ya ce "tambayar da nake yi ita ce "me ya sa APC ta manta da manufofin da aka kafa ta a kai?

    "Ban rabu da APC ba, amma APC ta bar ni," in ji tsohon gwamnan na jihar Kaduna.

    Daga nan ne gwamnan ya kore raɗe-radin da ake yi kan cewa zai shiga ɗaya daga cikin jam'iyyun adawa na ƙasar, musamman ma jam'iyyar PDP.

    "Ya kamata a sani cewa duk da ina APC ba haramun ba ne na ziyarci wasu abokaina da ke wasu jam'iyyun.

    "Amma babu ko shakka, abin da nake so a sani shi ne ba zan taɓa shiga PDP ba, har abada, na yanke wannan shawarar tuntuni, kuma tun daga wancan lokacin PDP ma ƙara lalacewa ta yi".

    Sai dai Malam Nasir El-Rufa'i wanda mutum ne mai yawan tayar da ƙura a siyasar Najeriya, ya tabbatar da cewa ba zai fita daga harkokin siyasa ba duk kuwa da cewa ya ja baya daga jam'iyyarsa ta APC.

    "Ban shirya fita daga siyasa ba, amma nan ba da jimawa ba dole zan nemi inda zan ci gaba da fafutikar cimma ƙudurorina na ci gaba, sai dai ina fatan APC za ta gyara lamurranta, ƙila idan ta gyara ire-iren mu za su sake duba matsayar da muka ɗauka."

  2. Cocin Vatican ya ce Fafaroma na samun sauƙi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Cocin Vatican ya bayyana cewa an fara ganin alamun sauƙi a rashin lafiyar Fafaroma Francis, wadda tun farko a yau aka bayyana cewa cutar ta yi tsanani.

    A sanarwar da ya fitar, cocin na Vatican ya ce a yanzu "cutar da ta shafi ƙodar fafaroman ba ta zama abin damuwa ba."

    Fafaroma ya kwashe kimanin kwana 11 ke nan a asibiti, inda likitoci suka ce yana fama da cutar sanyin haƙarƙari.

  3. Uba Sani da Nuhu Ribadu ba abokaina ba ne yanzu - El-Rufa'i

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i

    Asalin hoton, facebook/Nasir El-Rufa'i

    Bayanan hoto, Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya bayyana cewa 'a yanzu Uba Sani ba abokinsa ba ne' bayan abubuwan da ke faruwa baya-bayan nan.

    El-Rufa'i ya bayyana hakan ne a tattaunawar da ya gudanar da tashar talabijin ta Arise da yammacin yau Litinin.

    Bayan kammala wa'adinsa na shekara takwas a matsayin gwamnan jihar Kaduna, tsohon gwamnan na fuskantar bincike kan kuɗaɗe da ake zargin sun yi ɓatan-dabo a lokacin mulkinsa.

    Lamarin ya haifar da muhawara kasancewar thonon gwamnan na Kaduna, Nasir El-Rufa'i da gwamna mai ci Uba Sani sun kasance masu kusanci a tsawon shekara takwas na mulkin tsohon gwamnan.

    El-Rufa'i ya bayyana cewa aboki shi ne mutumin da zai kawo maka ɗauki ko a lokacin daɗi ko na tsanani.

    Ya ce "a yanzu Uba Sani da Nuhu Ribadu ba abokaina ba ne.

    "Na san cewa abokaina sun san cewa zan iya kai musu ɗauki a kowane lokaci," in ji tsohon gwamnan.

    A game da zargin da ake yi masa, El-Rufa'i ya ce bai taɓa cin ko sisi na kuɗaden da ba nashi ba a muƙaman da ya riƙe.

  4. Trump da shugaban Faransa, Macron na tattaunawa kan Ukraine

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Faransa, Emmanuel Macron da takwaran aikinsa na Amurka, Donald Trump na ganawa a fadar White House da ke birnin Washington.

    Hakan na zuwa ne yayin da aka cika shekara uku cif bayan samamen da Rasha ta ƙaddamar a kan Ukraine.

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Lokacin da suka zanta da manema labarai kafin a rufe ƙofa domin tattaunawa tsakanin shugabannin biyu, an tambayi Trump kan ko yana ganin ya kamata Ukraine ta sadaukar da wasu yankuna na ƙasarta a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar zaman lafiya.

    "Za mu ga abin da zai faru," in ji Trump. Ya ƙara da cewa "tattaunawa ce da aka fara a kwanan nan."

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Trump ya ce "ina ganin yaƙin (Ukraine) zai iya ƙarewa cikin ƙanƙanin lokaci, idan muka yi tsari mai kyau."

    "Idan kuwa ba mu yi tsari mai kyau ba to zai ci gaba...ba mu son hakan," in ji Trump.

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

  5. Ɓangaren Kwankwaso ba shi da hurumin korar mu daga NNPP - Kawu Sumaila

    Sanata Suleiman Abdurrahman Kawu Sumaila

    Asalin hoton, facebook/Kawu Sumaila

    Bayanan hoto, Sanata Suleiman Abdurrahman Kawu Sumaila

    Ƴan majalisar dokokin Najeriya da jam'iyyar NNPP reshen jihar Kano ta dakatar sun yi watsi da matakin jam'iyyar, tare da bayyana ta a matsayin wadda "ba ta halasta ba".

    A yau Litinin ne shugaban jam'iyyar NNPP a jihar ta Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa ya sanar da dakatar da ƴan majalisar huɗu daga jam'iyyar bisa zargin su da ayyukan "zagon ƙasa".

    A a tattaunawarsa da BBC, Sanata Kawu Sumaila ya ce "ita kanta wannan jam'iyyar da waɗanda suka yi sanarwar, kotu tana cajin su da cewa su ba halastattun shugabannin jam'iyya ba ne, don haka ba su da iko ko damar ɗaukar wannan mataki."

    A game da batun gayyatar da shugaban jam'iyyar ta NNPP ya bayyana a lokacin sanar da dakatar da ƴan majalisar, Sumaila ya ce "gayyata ce kawai ta zumunci... shi ke nan yanzu jam'iyya sai ta hana ka gayyaci mutane zuwa harkarka?"

    A martanin da suka fitar, ƴan majalisar, waɗanda suka haɗa da Sanata Suleiman Abdurrahman Kawu Sumaila, da Kabiru Alhassan Rurum, da Aliyu Sani Madakin Gini da kuma Abdullahi Rogo, sun ce dakatarwar ba wani abu ba ne face "yaudarar siyasa domin kawar da hankalin al'umma daga rashin kataɓus ɗin shugabancin jam'iyyar ɓarin Kwankwaso."

    Sanarwar ta ƙara da cewa jagoran jam'iyyar, Rabi'u Kwankwaso na amfani da "rarrabuwar kawuna a matsayin makami" wajen ci gaba da mallake jam'iyyar.

    "Shi ya sa suka ɓuge da bin wannan hanyar ta dakatarwa maras tushe.

    "Baya ga cewa wannan mataki haramtacce ne, wani yunƙuri ne kuma daga ɓarin jam'iyyar wanda aka riga aka sallama daga jam'iyyar NNPP, kuma bai ya da hurumi ko kaɗan na ɗaukar irin wannan mataki."

    Ƴan majalisar sun buƙaci al'umma su yi watsi da wannan kora, sannan suka ce suna nan cikin jam'iyyar inda za su yi duk mai yiwuwa "wajen ganin jam'iyyar ta amfani al'umma ba kawai son zuciyar Kwankwaso da muƙarrabansa ba."

  6. Bidiyon mota mai tashi sama da za ta shigo kasuwa

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Wani kamfanin ƙere-ƙeren da suka shafi jirgin sama a Amurka ya fitar da bidiyon mota mai tashi sama ta gwaji da kamfanin ya ƙera.

    Shugaban kamfanin da ake kira Alef Aeronautics, wato Jim Dukhovny, ya shaida wa BBC cewa yanzu haka dubban mutane sun yi odar motar, wadda ake sa ran za ta shiga kasuwa nan da ƙarshen shekarar 2025 ko farkon 2026.

  7. Mutane 7,000 sun mutu a rikicin Congo -

    congo

    Asalin hoton, Reuters

    Jami'ai a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo sun ce faɗan da ake a Gabashin ƙasar ya yi sanadin mutuwar mutane dubu bakwai.

    Firaiminista Judith Suminwa ta shaida wa taron da hukumar kare haƙƙin bil'adam ta MDD ke yi a Geneva cewa akwai wasu mutum kusan dubu 500 da ba su da wajen zama bayan lalata sansanonin ƴan gudun hijira da aka yi.

    Da yake jawabi a wajen taron da ake a Geneva, babban sakatare a MDD, Antonio Guterres, ya yi kira da a kawo ƙarshen zub da jinin da ake.

    Ya ce a Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo, sun ga yadda rikicin ya kazanta, da kuma irin yadda ake take haƙƙin ɗan adam wanda ƴan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda ke yi.

    Kungiyar ƴan tawayen M23 ta kwace manyan yankuna ciki har da birnin Goma da kuma Bukavu, abin da ya daɗa sanya fargabar cewa rikicin zai ƙara fadaɗa.

  8. Muna sa ran kawo ƙarshen yaƙi a wannan shekarar - Zelensky

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky
    Bayanan hoto, Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya bayyana cewa yana sa ran za a kawo ƙarshen yaƙin da ƙasarsa ke yi da Rasha a cikin wannan shekarar, bayan shekara uku da aka kwashe ana artabu tsakanin ɓangarorin biyu.

    Zelensky ya yi wannan kalamin ne sa'ilin da manema labarai suka tambaye shi game da fatansa ga Ukraine da al'ummarta.

    Muna sa ran kammala yaƙin a wannan shekarar," in ji shi, ya ƙara da cewa ƙasar baki ɗaya "ta sha wahala."

    Sai dai ya bayyana cewa ƙasar na buƙatar samun abin da za ta dogara da shi ta fannin tsaro, domin hana Rasha sake kai mata farmaki a shekaru masu zuwa.

    Ya ce shigar ƙasar cikin Tarayyar Turai da kuma ƙungiyar tsaro ta Nato nan kusa "zai taimaka ƙwarai da gaske".

    A baya-bayan nan Zelensky ya yarda cewa zai sauka daga muƙamin shugaban ƙasa idan aka amince Ukraine za ta shiga ƙungiyar Nato a madadin hakan.

    Rasha ta ce ba za ta taɓa amincewa da hakan ba.

  9. China za ta haramta tsawwala sadakin aure da bikin 'almubazzaranci'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin ƙasar China ta ci alwashin kawar da al'adar tsawwala sadaki da kuma bikin wadaka da kuɗi.

    Alwashin, wanda ya fito ta bakin jami'in gwamnati mai kula da lamurran yankunan karkara (Zhu Weidong), na zuwa ne bayan yawan aure da ake ɗaurawa a ƙasar ya ragu sosai a bara.

    Hukumomi na ganin cewa sadaki mai yawa na dubban daloli da ake yankawa da kuma kayan aure masu yawa da ake buƙata daga wurin maza, na daga cikin abubuwan da ke hana maza yin aure.

    Sai dai har yanzu hukumomin ba su ɗauki wani mataki kan dokar raba kaya bayan rabuwar aure, wadda ake ganin ta fifita maza.

  10. Gobara ta ƙone shaguna fiye da 100 a kasuwar Zamfara

    Gobara

    Asalin hoton, Ali Gashua

    Wata gobara a babbar kasuwar Gusau da ke jihar Zamfara ta laƙume aƙalla shaguna 103 a ɓangaren kayayyakin abinci masu saurin lalacewa da ke kasuwar.

    Duk da dai ba a gano dalilin faruwar gobarar ba, ɗaya daga cikin masu kashe gobarar ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa gobarar na da alaƙa da wutar lantarki inda ya ce gobarar ta kama ne jim kaɗan bayan kawo wuta a kasuwar.

    A cewarsu, gobarar ta soma ne da karfe 10:30 na daren Lahadi kuma ta shafe sa'oi ta na ci kafin ma'aikatan hukumar kashe gobar na jihar da na tarayya suka yi nasarar kashe ta da karfe biyun dare.

    Shugaban kungiyar masu sayar da kayan abinci da ke saurin lalacewa, Alhaji Inusa Saminu ya shaida wa jaridar ta Daily Trust cewa lamarin ya munana, kuma zuwa yanzu ba za su iya kirga asarar su ba sai dai ya ce sun kai miliyoyi.

    Ya ɗora alhakin ta'azarrar gobarar kan rashin isowar ma'aikatan kashe gobarar kan lokaci inda ya ce sun kira masu kashe gobarar na kusa da sai su ka ce musu motar ta lalace na tsawon watanni, wasu kuma su ka yi korafin motar ta su babu batir.

  11. Firaministan Iraq ya ce zai gina asibiti a Gaza

    Firaministan Iraq Muhammed Shia al-Sudani

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Iraq Muhammed Shia al-Sudani ya ce gwamnatinsa za ta gina asibiti a Gaza, a wani yunƙuri na nuna ƙin amincewa da shirin Donald Trump na fitar da Falasɗinawa daga yankin.

    Mista al-Sudani ya faɗi hakan ne a yayin da yake ganawa da wani likitan Iraqi Mohammed Taher Abu-Raghif wanda ya dawo daga Gaza inda yake kula da marasa lafiya da aka jikkata a yaƙin.

    Firaministan ya jinjina masa kan aikin da ya yi wanda ya ce shi 'abin alfahari ne ga ƴan Iraqi''.

    Wani jami'i ya ce za a gina asibitin ne tare da haɗin gwiwar ofishin jakandancin yankin Falasɗinu da ke Baghdad da hukumomin Gaza.

  12. Amurka da Ukraine sun kusa ƙulla yarjejeniyar haƙar ma'adanai

    Zelensky

    Asalin hoton, EPA

    Ukraine da Amurka na"matakin ƙarshe" na ƙulla yarjejeniyar haƙar ma'adanai, a cewar Mataimakin Firaministan Ukraine Olha Stefanishyna.

    A farkon watan nan ne Shugaba Zelensky ya ƙi amincewa da yarjejeniyar da za ta bai wa Amurkar damar shiga harkokin ma'adanan Ukraine a madadin tallafin soja da zai samu daga ƙasar.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafukan zumunta, Stefanishyna ya ce: "Tawagar Ukraine da ta Amurka na matakin ƙarshe game da yarjejeniyar.

    "Ana samun nasara a tattaunawar ƙwarai, inda tuni aka kammala dukkan wasu manyan ɓangarori. Muna da zimmar gamawa da ita cikin gaggawa.

    "Muna fatan jami'an Amurka da Ukraine za su amince kuma su saka hannu kan ta nan take domin nuna ƙoƙarinmu game da shekaru masu zuwa."

  13. Dusar ƙanƙara za ta lulluɓe biranen Japan, a cewar masana

    Masu hasasshen yanayi sun yi gargaɗin cewa wasu yankunan kasar Japan za su fuskanci ruwan dusar ƙanƙara a makonni masu zuwa.

    Dusar ƙanƙarar a baya ta binne garuruwa da dama a biranen Japan musamman a kudancin kasar.

    A yanzu haka yankin Aomori na binne cikin dusar ƙanƙarar da ta kai zurfin mita biyar, lamarin da ya janyo tsaiko ga matafiya da rufe makarantu, yayin da jami'an agajin gaggawa da jama'a ke aikin kwashe kankarar da ke rufin gidajensu.

    Arewacin Japan na daga wurare mafi zubar dusar kankara a duniya, sai dai akwai wurare da dama da suka fuskanci haka a lokacin hunturu.

  14. Nafdac ta rufe shagunan magani sama da 11,000 tare da kama mutum 40

    Hukumar Nafdac

    Asalin hoton, Nafdac

    Hukumar kula da ingancin magunguna da abinci ta Najeriya Nafdac ta ce ta rufe sama da shaguna 11,000 tare da kama mutum 40 a yaƙin da take yi da sayar da ƙwayoyin jabu.

    Da take yi wa 'yanjarida jawabi a ranar Lahadi, shugabar hukumar Farfesa Mojisola Adeyeye ta ce sun tsara samamen ne tun shekara ɗaya da ta wuce.

    Zuwa yanzu, Nafdac ta kai samame kasuwanni da dama ciki har da Idumota a Legas, da Ariaria a garin Aba, da Bridge Market a Onitsha a ranar 10 ga watan Fabrairu.

    Ta ce sun hari kasuwanni uku da ke rarraba kashi 80 cikin 100 na magunguna a Najeriya, kuma sun yi nasarar kamawa tare da ƙwace ƙwayoyin jabu da waɗanda ba a yi wa rajista ba.

    Farfesar ta kuma sun samu sama da mota 20 ta jabun magunguna a Aba, aƙalla 30 a Onitsha, da wasu 27 a kasuwar Idumota.

    "Abin da muka sa a gaba yanzu shi ne fara duba ɗaiɗikun shaguna domin gano masu karya doka da kuma waɗanda ba su da rajista," in ji ta.

  15. Wuta ta ƙone mutum huɗu ƙurmus cikin motar bas a Jigawa

    Wata mota tana ci da wuta a gefen titi

    Asalin hoton, Social Media

    Bayanan hoto, Wata mota tana ci da wuta a gefen titi

    Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum huɗu da kuma jikkatar wasu 10 bayan wata motar bas ta kama da wuta.

    Lamarin ya faru ne a ƙaramar hukumar Gwaram, kamar yadda kakakin rundunar Lawan Shiisu ya bayyana cikin wata sanarwa ranar Lahadi.

    "Lamarin ya faru ne ranar Asabar da misalin ƙarfe 4:00 na yamma lokacin da bas ɗin da ke ɗauke da fasinjoji 44 daga garin Zaki na jihar Bauchi ta kama da wuta," in ji shi.

    "Bayan ta isa kusa da makarantar Government Girls Unity Secondary School Gwaram, sai wutar ta mamaye motar sakamakon haɗuwa da ta yi da wata katifa da aka ɗaure a bayan motar."

    Wutar ta ƙone mutanen ne duka mata ƙurmus ta yadda ba za a iya gane su ba, a cewarsa. Waɗanda suka ji raunika kuma, nan take aka garzaya da su asibitin Gwaram Cottage.

    Ya ƙara da cewa daga cikin fasinjojin, 25 manya ne, da kuma yara 19.

  16. Waɗanne jam'iyyu ne za su kafa gwamnati a Jamus?

    Friedrich Merz

    Asalin hoton, Reuters

    Jam'iyyar 'yan ra'ayin riƙau da Friedrich Merz ke jagoranta ta lashe zaɓe a Jamus ta yi nasara ne kashi 28.6 cikin 100.

    Bayan kammala ƙirga ƙuri'u, jam'iyyar Alternative for Germany (AfD) ce ta zo ta biyu, yayin da Social Democrats (SPD) ta zo ta uku, sai kuma Greens ta huɗu.

    Ƙananan jam'iyyu biyu da suka kusa cin kashi 5 cikin 100 sun gaza samun kujera ko ɗaya a majalisa.

    Ganin cewa jam'iyyu biyar ne kawai ake ganin za su iya haɗa kai da Mista Merz da wata jam'iyya ɗaya wajen kafa gwamnati, ana tunanin jam'iyyar su Olaf Sholz mai barin gado ce Social Democrats (SPD) za ta shiga gwamnatin haɗakar.

  17. An kama jagoran ƙungiyar tawaye a Nijar Mahmoud Sallah - Rahotonni

    Mahmoud Sallah

    Asalin hoton, Social Media

    Rahotonni daga Nijar na cewa hukumomi sun kama shugaban ƙungiyar tawaye ta Patriotic Liberation Front (FPL), Mahmoud Sallah.

    Kafar yaɗa labarai ta Air Info Agadez ta ruwaito cewa an kama shi ne a yankin Gatroun na ƙsar Libya.

    Rahoton ya ƙara da cewa jami'an tsaron Libya ne suka kama shi tare da mabiyansa biyar a ranar Lahadi.

    "Mahmoud Sallah sananne wajen adawa da gwamnatin sojan Nijar, wadda kuma yaƙa ta kowace irin hanya," in ji rahoton.

    Tuni gwamnatin ƙarƙashin Janar Tchiani ta ƙwace Sallah 'yancinsa na zama ɗan ƙasa.

    Ƙungiyar FPL ta ce tana gwagwarmayar nema a saki hamɓararren Shugaba Mohamed Bazoum ne da kuma "dawo da aiki da kundin mulkin ƙasa".

    A baya ta yi barazanar dasa bam a matatun man fetur na ƙasar da ke a Agadem a gabashin Nijar.

  18. Shugaban Jamus mai jiran gado ya caccaki Amurka

    Friedrich Merz

    Asalin hoton, Reuters

    Mutumin da ake ganin shi zai zama shugaban gwamnatin Jamus nan ba da jimawa ba ya ce abu muhimmi da zai mayar da hankali a kai shi ne hadin kan ƙasashen Turai.

    Friedrich Merz ya ce suna buƙatar hakan ne domin rage dogaro kan Amurka, wadda ya ce ta "daina damuwa da makomar nahiyar Turai".

    Mista Merz ya ce dole ne Turawan su dogara da kansu, yana mai dasa ayar tambaya kan makomar kungiyar tsaro ta NATO.

    Ya kuma nuna fushi da sukar matakin jam'ian Amurka na tsoma baki a harkokin Jamus bayan Elun Musk ya bayyana goyon baya ga jam'iiyar adawa ta AFD.

  19. Ba za mu ci gaba da tattaunawa ba sai an sako Falasɗinawa 600 - Hamas

    Falasɗinawa

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Wasu Falasɗinawa kenan suke jiran a sako 'yan'uwansu daga gidajen yarin Isra'ila

    Ƙungiyar Falasɗinawa ta Hamas ta ce ba za ta ci gaba da tattaunawar zaman lafiya da Isra'ila ba har sai ta sako fursunoni Flasdinawa sama da 600 kamar yadda aka cim ma yarjejeniya tun da fari.

    Isra'ila ta jinkirta sakin Falasdinawa sama da 600 a ranar Asabar bayan Hamas ta mika wa kungiyar agaji ta Red Cross Isra'ilawa shida masu rai da take garkuwa da su.

    Firaminista Benjamin Netanyahu ya ce sun ɗauki matakin ne "har sai an tabbatar da sakin rukuni na gaba na mutanen da ake garkuwa da su, kuma sai Hamas ta daina gabatar da su a gaban 'yankallo".

    Ya kuma yi barazanar a kowanne lokaci Isra'ila ka iya komawa yaƙin da suka kwashe sama da shekara suna gwabzawa a Zirin Gaza.

    A farkon watan Maris ne wa'adin z farangoko na yarjejeniyar tsagaita wutar zai ƙare.

  20. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake haɗuwa a sabon shafin labarai kai-tsaye na ranar Litinin - mande tushen aiki.

    Ni ne Umar Mikail zan jagoranci kawo rahotonnin game da abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman a Najeriya da Nijar da maƙwabtansu.

    Za mu yi hakan ne bisa kulawar Usman Minjibir.