Gwamnatin Neja ta rufe duka makarantun jihar
Gwamnatin jihar Neja da ke tsakiyar Najeriya ta sanar da rufe duka makarantun da ke faɗin jihar sakamakon sace wasu ɗaliban makarantar St. Mary mai zaman kanta a garin Papiri na karamar hukumar Agwara.
Gwamnan jihar Umaru Bago ne ya sanar da haka yayin da yake zantawa da manema labarai a birnin Minna, fadar gwamnatin jihar.
Matakin na zuwa ne bayan rufe makarantun a jihohin Filato da Katsina.
Umaru Bago ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da ceto ɗaliban tare da maido su cikin kwanciyar hankali.
Gwamnan ya kuma bayyana lamarin da ''abin takaici da bakin ciki, da ya girgiza al'ummar jihar''.