Al'ummar Gabon na zaɓen sabon shugaban ƙasa
An buɗe rumfunan zaɓe a Gabon, yayin da al'ummar ƙasar za su zaɓi sabon shugaban ƙasar, kusan shekara biyu bayan juyin mulkin da ya hamɓarar da tsohon shugaban ƙasar Ali Bongo.
Shugaban gwamnatin mulkin sojin ƙasar, Brice Oligui Nguema - wanda ya alƙawarta miƙa mulki ga farar hula - na daga cikin mutanen da ke takarar, kuma alamu na nuna cewa shi ne zai yi nasara a zaɓen.
Yana fafatawa da wasu ƴantakara bakwai, ciki har da tsohon firaministan ƙasar, Alain Claude Bilir-By-Nze.
Juyin mulkin da ka gudanar a ƙasar - da ke tsakiyar Afirka - a 2023, ya kawo ƙarshen mulkin iyalan Bongo na kusan shekara 60 a ƙasar.