Iran da Amurka sun ce 'akwai haske' bayan tattaunawarsu kan nukiliya
Iran da Amurka sun kammala zagaye na farko na tattaunawarsu kan shirin Iran na makamin nukiliya, wanda aka yi a ƙasar Oman.
Ƙasashen biyu sun bayyana cewa 'akwai alamar haske' bayan tattaunawar, wadda aka yi domin samar da yarjejeniya kan dakatar da shirin Iran na samar da nukiliya.
Donald Trump ne ya fice daga yarjejeniyar Iran da ƙasashen duniya a 2018, inda ya ce zai jagoranci tsara wata yarjejeniyar daban da "za ta fi dacewa."
Tattaunar ta farko, wadda aka yi awa biyu da rabi ana yi, rahotanni sun ce an gudanar da ita cikin girmamawa, sannan ta buɗe ƙofar shiga zagaye na biyu.
Wakilin Iran a taron, ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araghchi ya ce, "ina tunani tattaunawar ta yi kyau domin an yi ta ne cikin girmamawa ba tare da cin mutunci ba," in ji shi a tattaunawarsa da talabijin na Iran.