Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 06/01/2026.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 06/01/2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi, Aisha Babangida, Abdullahi Diginza da Ahmad Bawage

  1. Mutum 25 sun mutu bayan kifewar kwale-kwalen ƴan ci-rani a tekun Gambia

    Gwamnatin Gambia ta tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 25 bayan wani kwale-kwale da ke ɗauke da ’yan ci-rani ya kife a gaɓar tekun ƙasar, yayin da ake shirin shiga sabuwar shekara.

    Jami’an tsaro sun ce kwale-kwalen na ɗauke da fiye da mutum 200, kuma har yanzu ba a gano dayawa daga cikinsu ba.

    Rahotanni sun nuna cewa yawancin waɗanda ke cikin kwale-kwalen matasa ne daga ƙasashen Yammacin Afirka, masu kasadar ketare teku domin neman shiga Turai, galibi ta hanyar tsibiran Canary na ƙasar Sifaniya.

    Ana yawan yin irin wannan tafiya ne da kwale-kwale marasa inganci da ke cike da mutane fiye da ƙima, lamarin da ke haddasa haɗurra masu muni.

    Shugaban Gambia, Adama Barrow, ya bayyana cewa ƙasar na cikin jimami sakamakon wannan mummunan haɗari.

  2. Ƴan Venezuela sun yi zanga-zangar neman sakin Maduro

    Dubban magoya bayan shugaban Venezuela, Nicolás Maduro, sun mamaye titunan babban birnin ƙasar Caracas, suna nuna fushinsu kan kama shi da Amurka ta yi tare da buƙatar a dawo da shi gida.

    Magoya bayan shugaban sun ce matakin da Amurka ta ɗauka ya saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa.

    Magoya bayan gwamnatin, musamman masu ra’ayin neman sauyi, sun bayyana cewa har yanzu suna cike da ɓacin rai kan abin da suka kira tsoma bakin Amurka a harkokin cikin gidan Venezuela a ƙarshen mako.

    A yayin sauraron ƙarar da ake yi masa a wani kotu a birnin New York, Nicolás Maduro ya jaddada cewa har yanzu shi ne halastaccen shugaban Venezuela inda ya bayyana kama shi da sojojin Amurka suka yi a ranar Asabar a matsayin “sace shi”.

    Maduro da matarsa, Cilia Flores, wadda ita ma aka kama, sun musanta dukkan tuhumar da ake yi musu ta laifukan hada-hadar miyagun ƙwayoyi da ta’addanci.

    A halin yanzu, an rantsar da mataimakiyarsa a matsayin shugabar riko ta Venezuela, yayin da rikicin siyasar ƙasar ke kara kamari.

  3. Yadda APC ke neman Nyesom Wike ya ajiye muƙamin Ministan Abuja

    Zazzafar cacar-baka ta kaure tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, Nyesom Wike, da Sakataren Jam'iyyar APC, Ajibola Bashiru, lamarin da ya kai ga Sakataren jam'iyyar kiran da Wike ya sauka daga muƙaminsa na minista, bisa hujjar cewa ba ɗan jam'iyyar APC ba ne.

    Wannan dai na zuwa ne bayan Wike ya gargadi Sakataren da ya tsame hannunsa daga siyasar jihar Ribas, sakamakon sanarwar da shugabancin APC suka fitar cewa Gwamna Siminalayi Fubara ne jagora kuma shugaban jam'iyyar mai mulki a jihar.

    Rikicin ya faro ne tun bayan ziyarar da Sakataren APC da tawagarsa suka kai wa Gwamna Siminalayi Fubara a jihar Ribas, inda daga bisani Bashiru ya sake jaddada tsarin jam'iyyar cewa kowane gwamna shi ne jagoran jam'iyyar a jiharsa.

  4. Wane tasiri gwamnoni ke yi wajen cin zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya?

    Ƴan Najeriya na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan yadda wasu gwamnonin jam'iyyun hamayya ke tururuwar komawa jam'iyyar APC mai mulki.

    Wasu na ganin gwamnonin na komawa ne domin kwaɗayin samun tikitin takarar kujerunsu da kuma yiwuwar sauƙin cin zaɓukansu.

    To sai dai wasu na zargin cewa jam'iyya mai mulkin ce ke zawarcinsu da nufin samun sauƙin lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

    Zargin da APC ta sha musantawa a lokuta daban-daban.

    To amma gwamnonin na da tasiri wajen nasarar shugaban ƙasa a zaɓukan Najeriya?

  5. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyarmu, Barkanmu da war haka, da fatan muna cikin ƙoshin lafiya.

    Kamar kullum, a yau ma wannan shafi na Kai Tsaye zai kawo rahotanni da labarai na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sauran kasashe makwabta.

    Sai ku ci gaba da bibiyar mu domin sanin halin da duniya take ciki a yau Talata.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.