Gwamnatin Ghana ta roƙi ma'aikatan lafiya da ungozoma su janye yajin aiki
Gwamnatin Ghana ta buƙaci ma'aikatan lafiya da ungozoma da ke yajin aiki tun ranar 2 ga Yuni da su janye yajin aikin wanda yanzu ya shiga mako na biyu.
Yajin aikin in ji gwamnatin ƙasar na haddasa cikas sosai ga tsarin kula da lafiya a ƙasar.
Yajin aikin ya ƙara ta'azzara ne a ranar Litinin lokacin da ma’aikatan suka janye ayyukansu gaba ɗaya daga cibiyoyin lafiya.
Rahotannin kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun nuna cewa yajin aikin, wanda ya samo asali daga rikici kan albashi, ya jefa asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya cikin wani hali na rudani da cunkoso da kuma gazawa.
Gwamnatin ta roƙi ma’aikatan da su yi sassauci tare da janye yajin aikin domin ceton rayukan marasa lafiya da ke cikin matsanacin hali.