Afirka ta Kudu na bincike kan hare haren da ake kai wa ƴan Ghana a ƙasar
Gwamnatin Ghana ta ce hukumomin Afirka ta Kudu sun kaddamar da bincike kan jerin hare-haren da ake kaiwa na ƙyamar baƙi a kan 'yan Ghana da ke zaune a Afirka ta Kudun.
A kwanakin nan hotunan bidiyo da ke nuna yadda ake cin zarafin 'yan Ghana a Afirka ta Kudu sun yaɗu sosai.
Harin kyamar baki abu ne mai sarkakiya - wanda matsala ta tattalin arziki, da yaɗa bayanai na ƙarya, da sauran wasu matsaloli ke kara rura wutarsa.
Ana ta samun ƙaruwar zanga-zanga da tashin hankali, inda ake harar baƙi waɗanda ba 'yan ƙasar ta Afirka ta Kudu ba, yayin da ake shirin gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomi nan gaba cikin shekarar nan.
A watan da ya gabata Najeriya ta yi kira ga 'yan kasarta da su yi kaffa-kaffa, sakamakon wata zanga-zanga kan baƙin haure da ta rikiɗe ta zama tashin hankali.