Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman bayanai dangane da yaƙin Iran da ma sauran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na 23/04/2026

Taƙaitattu

  • Sojojin Najeriya sun kashe gomman ƴan bindiga da lalata jiragen ruwansu a Tafkin Chadi
  • Trump ne zai yanke shawara kan lokacin da za a ƙare yaƙin Iran- White House
  • Wane ne Sarki Sulaimanu, Sarkin Kano na farko a tarihi?
  • 'Yawan kuɗin takardun neman takara na APC illa ne ga cigaban ƙasa'
  • PSG na son Fernandes, Barca na harin Silva da Neto
  • Iran na da tarin sindarin uranium - amma me ya sa ba za ta iya mallakar makamin nukiliya ba?

Rahoto kai-tsaye

Aisha Aliyu Jaafar, Isiyaku Muhammad da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Afirka ta Kudu na bincike kan hare haren da ake kai wa ƴan Ghana a ƙasar

    Gwamnatin Ghana ta ce hukumomin Afirka ta Kudu sun kaddamar da bincike kan jerin hare-haren da ake kaiwa na ƙyamar baƙi a kan 'yan Ghana da ke zaune a Afirka ta Kudun.

    A kwanakin nan hotunan bidiyo da ke nuna yadda ake cin zarafin 'yan Ghana a Afirka ta Kudu sun yaɗu sosai.

    Harin kyamar baki abu ne mai sarkakiya - wanda matsala ta tattalin arziki, da yaɗa bayanai na ƙarya, da sauran wasu matsaloli ke kara rura wutarsa.

    Ana ta samun ƙaruwar zanga-zanga da tashin hankali, inda ake harar baƙi waɗanda ba 'yan ƙasar ta Afirka ta Kudu ba, yayin da ake shirin gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomi nan gaba cikin shekarar nan.

    A watan da ya gabata Najeriya ta yi kira ga 'yan kasarta da su yi kaffa-kaffa, sakamakon wata zanga-zanga kan baƙin haure da ta rikiɗe ta zama tashin hankali.

  2. Trump ne zai yanke shawara kan lokacin da za a ƙare yaƙin Iran- White House

    Fadar gwamnatin Amurka ta ce babu wani wa'adi na kawo ƙarshen dakatar da buɗe wuta da Iran, wanda Donald Trump ya tsawaita ranar Talata da daddare.

    Sakatariyar yaɗa labaran fadar, Karoline Leavitt ta shaidawa manema labarai cewa shugaba Trump, zai yanke shawara kan lokacin da za a kare yakin.

    Haka kuma ta kafe cewa datse tashoshin jiragen ruwa na Iran da Amurka ta yi na samun nasara, ta hanyar yi wa tattalin arzikin Iran din abin da ta kira ''KANSHIN MUTUWA''.

    Wakiliyar BBC ta ce Amurka na fata ne na ganin datsewar da ta yi wa Mashigar Hormuz ta sa tattalin arzikin Iran ya jigata yadda hakan zai sa Iran din ta je teburin tattaunawar.

    Shugaban kasar Iran din Masoud Pezeshkian, ya bayyana wannan datsewa a matsayin daya daga cikin manyan abubuwan da suka haifar da tarnaki ga tattaunawar zaman lafiya.

    Ya ce kasarsa a shirye take a tattauna, amma ya zargi Amurka da - da kalamai na munafurci da ba sa karewa.

    A gefe guda kuma, Iran ɗin ta sha alwashin ba za ta sake buɗe Mashigar Hormuz ba.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafinmu na BBC Hausa kai-tsaye, barkanmu da safiyar yau Alhamis, inda yau ma kamar kullum za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya.

    Za kuma ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa, da kuma kallon bidiyo.

    Da fatan za ku kasance tare da mu.