Jami'an kashe gobara na fafatawa da gobarar daji a Faransa

Asalin hoton, Frank Desprez / SDIS 77 via EPA
Gobarar daji da ke ci gaba da bazuwa a wani daji da ke kudancin birnin Paris ta mamaye kusan murabba’in kilomita ashirin, yayin da jami’an kashe gobara ke fatan shawo kanta a yau.
Ministan harkokin cikin gidan Faransa ya ce an kama mutum biyu bisa zargin haddasa gobarar da gangan.
Ɗaya daga cikinsu matashi ne mai shekara 18, wanda rahotanni suka ce an kama shi ɗauke da abin kunna wuta, yayin da hannayensa ke cike da toka.
A faɗin ƙasar, an kama mutane 59 bisa zargin haddasa gobara da gangan ko kuma sakaci.
A karon farko a yankin Paris, an tura jiragen sama na musamman da jirage masu saukar ungulu masu zubar da ruwa domin taimakawa wajen dakile gobarar.





















