An kashe ƴan jarida uku a wani harin da Isra'ila ta kai a Gaza
Ma’aikatan bayar da agajin gaggawa sun ce an kashe falasɗinawa ƴan jarida guda uku a wani harin da Isra'ila ta kai a tsakiyar Gaza.
Hukumar kare haƙƙin farar hula a Gaza ta ce an kashe ƴan jaridan ne bayan an kai wa motarsu hari a yankin al-Zahra inda ta bayyana sunayensu da Mohammed Salah Qashta da Anas Ghneim da kuma Abdul Raouf Shaat. An fahimci cewa suna aiki ne da wata ƙungiyar agaji ta Masar.
Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kai hari kan wasu da ake zargi da yin amfani da wani jirgi mara matuki da ke da alaka da Hamas... ta hanyar da ke barazana ga dakarunta. Inda ta ƙara da cewa tana kan gudanar da bincike kan lamarin.
Ma'aikatar lafiya ta Hamas ta sanar da cewa, an kashe wasu mutane takwas, biyu daga cikinsu yara kanana da makaman atilare na Isra'ila a Gaza a ranar Laraba.
Likitoci sun ce mutane uku ciki har da wani yaro ɗan shekara 10, sun mutu sakamakon Harbin da tankokin yaƙin Isra'ila suka yi a wani wuri a tsakiyar Gaza, kuma wani yaro dan shekara 13 da wata mata sun mutu sakamakon harbin da sojojin Isra'ila suka yi a kudancin yankin Khan Younis, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Aƙalla Falasdinawa 466 ne aka kashe a Gaza tun bayan da aka fara tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas a ranar 10 ga Oktoba, a cewar ma'aikatar lafiya.