Muna tattaunawa da Oman game da mashigar Hormuz - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Iran ta ce tattaunawar da take yi da Oman kan sababbin tsare-tsaren gudanar da zirga-zirga a Mashigar Hormuz na tafiya yadda ya kamata.
Sai dai babban jami'in tsaro na Tehran, Mohammad Bagher Zolghadr, ya yi gargaɗin cewa ba za a sake buɗe mashigar ruwan ba har sai Amurka ta amince da wasu sharuɗɗa guda shida.
Daga cikin sharuɗɗan akwai sassauta takunkumin tattalin arziki da aka ƙaƙaba wa Iran, da biyan diyya kan asarar yaƙi, da kuma kawo ƙarshen toshe tashoshin jiragen ruwan ƙasar da Amurka ke yi.
Wakilin BBC ya ce abin da muka ji daga shugaban tsaron shi ne sai an cimma wadannan bukata idan har za a sake bude Mashigar Hormuz Tun da farko, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya ce Iran da Oman sun yi kusa sosai da cimma yarjejeniya kan wata sabuwar hanya ta zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar ta Hormuz.
A halin da ake ciki kuma, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta ce Iran ta kai harin makami mai linzami kan ɗaya daga cikin jiragen ta na ruwa na dakon mai.







