Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 18/07/2024.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail da Usman Minjibir

  1. Masana sun yi gargaɗi kan barazanar Maleriya

    Masana Kimiyya sun yi gargadin cewa rayuwar miliyoyin mutane na cikin hadari idan ba a dauki matakin gaggawa ba wajen dakatar da zazzabin Malariya da ke bijirewa magani wanda kuma ke yaduwa a nahiyar Afirka kamar yadda ya yi shekaru 50 da suka wuce lokacin mace-macen da ya ninka har sau uku.

    Kwayoyin Malariya wadanda ke bijirewa muhimmin maganin na artemisinin, yanzu ba su a gabashin Afirka.

    Bijirewa magungunan cutar ta malariya yanzu ya karu a wasu yankuna daga kashi daya cikin 100 zuwa fiye da kashi 20 cikin 100.

    Wasu masana kimiyya sun ce daga kasashe 10, yaduwar irin nau'in wannan cuta ya wuce kima ba tare daukar matakin da ya dace ba.

  2. Gwamnatin sojin Nijar ta rage farashin fetur

    Gwamnatin sojin Nijar ta sanar da rage farashin man fetur a fadin ƙasar.

    Gwamnatin ta rage farashin fetur ne ƙasa daga CFA 540 zuwa CFA 499, haka ma an rage farashin dan dizel zuwa CFA 618 daga CFA 668.

    Gwamnatin ƙasar ta ce matakin zai soma aiki ne daga ranar 23 ga watan Yuli.

    Gwamnatin sojin Nijar ta ce manufar rage farashin shi ne rage wa ƴan ƙasa raɗaɗi musamman samun sauki kan farashin sufuri da na kayayyakin masarufi na yau da kullum.

    Sai dai masu nazari kan al'amuran yau da kullum na ganin ya kamata gwamnati ta ɗauki mataki na tabbatar da ganin 'yan kasuwa a kasar sun sauko da farashin kayayaki.

  3. Biden na shan matsin lamba ya janye takararsa

    Shugaba Biden na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga 'yan jam'iyarsa ta Democrats a kan ya ajiye batun sake neman takara a zaben watan Nuwamba da za a yi.

    Jaridar Washington Post ta rawaito cewa tsohon shugaban Amurka Barrack Obama wanda har yanzu yake da karfin fada a ji ya shaida wa kawayensu cewa akwai bukatar Mr Biden ya yi nazari sosai a kan takararsa, domin yiwuwar samun nasararsa kan Donald Trump na kara yin rauni.

    Sauran manyan 'yan jam'iyar Democrats ma sun ba wa Mr Biden wannan shawara a fili ko a a sirrance.

    Shugaban kasar mai kimanin shekaru 81 a duniya ya shafe yinin yau yana kebe a gidansa da ke Dilaware bayan da gwaji ya tabbatar da ya kamu da cutar Korona.

  4. Netanyahu ya yi watsi da shawarar gina asibiti a Gaza

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, ya soke umarnin da ministan tsaron kasar ya bayar na gina asibiti a Isra'ila don kula da yara a Gaza.

    A ranar Laraba Yoav Gallant, ya sanar da cewa ya shaida wa sojojinsu cewa a gina asibitin wucin gadi a kusa da iyakar Isra'ila da yankunan Palasdinawa.

    Amma sai gashi a yau, ofishin Firaministan ya ce bai amince da gina asibitin ba. Mr Gallant, ya ce ya bayar da wannan damar ce saboda shawarar da aka tsara tun da farko cewa za a rinka kai yaran Gaza da suka ji rauni kasashen waje don a yi musu magani amma matakin ya makale a ofishin Firaminista.

    Ma'aikatar tsaron ta zargi Netanyahu da sanya siyasa a al'amuran da suka shafi rayuwar jama'a.

  5. CBN ya sayar wa ƴan canji dala kan farashin N1,450

    Babban Bankin Najeriya ya sayar da dala ɗaya kan N1,450 ga ƴan canji masu lasisi a ƙasar.

    Babban Bankin ya sanar da matakin ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

    Ana ganin matakin zai samar da wadatar dala a Najeriya wanda kuma zai sa farashinta ya sauka kan naira.

    Ɗaya daga cikin shugabannin ƴankasuwar ƴancin ya shaida wa BBC cewa a ranar Alhamis an yi cinikin dala kusan 1,630, amma bayan sanar da matakin farashinta ya fara sauka

    Babban Bankin ya buƙaci ƴan canjin su saka kuɗi a bankin domin samun dalar cikin farashin mai sauƙi tare da umartar su sayar da sauƙi a kasuwa.

  6. NLC ta amince da tayin albashin N70,000 mafi ƙanƙanta

    Shugabannin ƙungiyar ƙwadago ta NLC sun sanar da amincewarsu da naira 70,000 a matsayin albashi mafi ƙanƙanta ga ma'aikatan ƙasar.

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ne ya amince da sabon albashin a ganawarsa da wakilan ƙungiyoyin ƴan ƙwadago na ƙasar a ranar Alhamis.

    Wannan na zuwa ne bayan kwashe tsawon lokaci ana taƙaddama tsakanin ƴan ƙwadago da gwamnatin Najeriya game da sabon albashin mafi ƙanƙanta ga ma'aikata.

    Shugaban NLC Joe Ajaero ya ce sun amince ne da tayin N70,000 saboda akwai abubuwan da ke ƙunshe da ya kira na ƙarfafa guiwa.

    Ƙungiya ta ce abin da ya ƙara ƙarfafa mata guiwa na amincewa da tayin shi ne alƙawalin da shugaban ƙasar ya ɗauka na sake duba albashin duk bayan shekara uku maimakon shekara biyar, kamar yadda mataimakin shugaban Kabiru Adamu Minjibir ya shaida wa manema labarai a fadar shugaban ƙasa.

    "Sannan gwamnati za ta bayar da manyan bas bas masu ɗaukar mutum 100 wanda zai rage wa ma'aikata wahalar tafiye-tafiye," in ji shi.

    Tun janye tallafin mai da gwamnatin Bola Tinubu ta yi, ta shiga takun-saka da ƙungiyoyin ƙwadago, inda suka nemi ƙarin albashi da ya zarta kashi 300 cikin 100 sakamakon tsadar rayuwa da janye tallafin ya jefa ƴan Najeriya.

  7. Starmer ya sha alwashin farfaɗo da dangantaka tsakanin Birtaniya da EU

    Sabon Firaministan Birtaniya, Sir Kier Starmer, ya sha alwashin sake farfaɗo da dangantakar da ke tsakanin Birtaniya da ƙungiyar Tarayyar Turai.

    Ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya yi a wajen wani babban taro da aka yi a Ingila.

    Da yake jawabi ga sauran shugabannin da suka hallara a fadar Blenheim don halartar taron shugabannin siyasa na nahiyar Turai.

    Keir Starmer, ya ce yana son ya sake gano inda muradunsu suka zo ɗaya, wanda shi ne ginshikin kasancewarsu 'yan nahiyar Turai.

    Ya ce yana kuma so su yi aiki kafaɗa da kafaɗa a fannoni daban-daban kamar samar da makamashi marar gurɓata muhalli da tallafa wa Ukraine da kuma magance matsalar baƙin haure.

  8. Kotu ta tuhumi matashin da ya cinna wa mutane wuta a masallaci a Kano

    Wata babbar kotun shari'ar Musulunci ta karanta wa Shafi'u Abubakar matashin da ake zargi da cinna wa mutane wuta a masallaci tuhume-tuhume guda huɗu da ake yi masa waɗanda suka haɗa da;

    • Zargin sanadiyyar kisan mutum 23 da gangan ta hanyar cinna musu wuta a masallaci a garin Gadan wanda aka fi sani da Larabar Abasawa cikin ƙaramar hukumar Gezawa.
    • Yunƙurin kisan wasu mutum biyu a ranar 15 ga watan Mayu 2024 a garin Gadan.
    • Raunata wasu mutane ta hanyar watsa musu fetur a masallaci lamarin da ya yi sanadin haifar musu da munanan raunika.
    • Ƙone masallaci da abubuwan da suke ciki alƙalin kotun Ustaz Halhalatul-khuza'i Zakaria ya tambayi Shafi'u Abubakar wanda ake tuhuma ko ya fahimci tuhumar sai ya amsa da cewa "E" ya fahimta tare da tabbatar da cewa "lalle haka abin yake ya aikata".

    Babbar kotun Shari'ar MusUluncin ta ɗage zamanta zuwa ranar 1 da 2 ga watan gobe na Agustar 2024, inda ake fatan kotun zata yi masa hukuncin kamar yadda masu kara suka nema.

  9. An sake zaɓar Von der Leyen shugabar hukumar EU

    Majalisar dokokin Tarayyar Turai ta sake zaɓar Ursula Von der Leyen, a matsayin shugabar hukumar Tarayyar Turai.

    Ms Von der Leyen za ta jagoranci hukumar har zuwa shekara biyar masu zuwa.

    Da take jawabi bayan zaɓen, shugabar hukumar ta ce kare martabar dimokradiyyar Turai shi ne babban abin da za ta sanya gaba.

    Ta ce ''muna aiki tare don karfafa nahiyar Turai, muna aiki a kan batutuwan da suka shafi ci gaba da gogayya a ciki tattalin arzikinmu''.

    Fiye da mambobin Majalisar 400 daga cikin 720 ne suka zaɓi Ms von der Leyen ciki har da waɗanda suka fito daga ɓangaren masu son kawo sauyi da na ɓangaren masu matsakaicin sassaucin ra'ayi.

    Ta dai yi alƙawarin bai wa EU babbar dama wajen kare kanta daga dukkan wasu ƙalubale musamman na tsaro, tare da tabbatar da cewa ƙasashe mambobin hukumar za su rage fitar da iskar da ke gurɓata muhalli da kashi 99 cikin 100 nan da 2040.

  10. Ƴan majalisar wakilai sun sadaukar da rabin albashinsu na tsawon wata shida

    Ƴan majalisar wakilan Najeriya sun amince da a zabtare kaso 50 na albashinsu na tsawon watanni shida a wani mataki na nuna tausayawa ga yanayin matsin tattalin arziƙi da yunwa da ƴan Najeriya ke ciki a halin yanzu.

    Wannan dai ya biyo bayan amincewa da gyaran ga buƙatar da mataimakin shugaban majalisa, Benjamin Kalu ya yi na buƙatar ƴan majalisar da su sadaukar da kaso 50 na albashin nasu na naira 600,000 da suke karɓa.

    Hon Benjamin Kalu ya ce zabtare albashin nasu zai taimaka wa gwamnati wajen sauƙaƙa wa ƴan ƙasar rayuwarsu.

    Hakan na nufin ƴan majalisar wakilan guda 360 za su tara tsabar kuɗi har naira miliyan 648 wato fiye da rabin naira biliyan ɗaya, idan aka zabtare musu naira miliyan 108 a duk wata.

  11. Ƙungiyoyin SSANU da NASU sun yi zanga-zanga a Abuja

    Kungiyoyin ma’aikatan jami’o'in Najeriya, waɗanda ba malamai ba da ake kira da (SSANU da NASU) sun gudanar da wata zanga-zanga saboda riƙe musu kuɗin albashinsu na watanni.

    Masu zanga-zangar sun fara ne daga filin taro na Unity Fountain a Abuja babban birnin ƙasar.

    Ma'aikatan sun zargi gwamnatin ƙasar ta riƙe musu albashinsu na watanni huɗu a lokacin da suka yi yajin aki a 2022, da kuma yarjejeniyar 2010 da suka cimma da gwamnatin wadda har yanzu ba a cika musu ba.

  12. Taron jam'iyyar kwamunisanci ya tashi ba tare da cimma matsaya ba

    An kammala wani muhimmin taron jam'iyyar kwamunisanci a Beijing, ba tare da ɓullo da yadda shugabannin China za su yi ƙoƙarin warware matsalar tattalin arzikin da ƙasar ke fuskanta ba.

    Cikin sanarwar bayan taron, jam'iyyar ta yi alƙawarin ɓullo da sabbin sauye-sauye, to amma ba a bayar da cikakken bayani kan sauye-sauye ba.

    Tattalin arzikin China na fuskantar babbar matsala, ciki har da bashin da ya yi wa ƙananan hukumomi katutu da kuma yadda kasuwanni ƙasar ke cikin wani yanayi marar kyau.

    Ana dai gudanar da irin wannan taro ne sau ɗaya cikin shekara biyar, don tattauna makomar tattalin arzikin ƙasar.

  13. Sojojin Najeriya sun gano makamai masu yawa a Barikin Ladi

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun gano makamai masu yawa na zamani da kuma ƙirar gida a gundumar Fann da ke yankin ƙaramar hukumar Barikin Ladi a jihar Filato.

    Cikin wata sanarwa da sojojin suka fitar sun ce sun ƙaddamar da samame a ƙauyukan gundumar ne bayan da wasu ɓata-gari suka kashe wani jami'in shige da fice a lokacin da jami'an tsaro ƙarƙashin rundunar Operation SAFE HAVEN ke sintiri a yankin.

    An ce ɓata-garin sun kashe jami'in a lokacin da yake duba motarsu wadda aka yi zargin sun ɗauko makamai a cikinta.

    Bayan haka ne jami'an sojojin suka ƙaddamar da samame da nufin gano makamai tare da kama mutanen da ake zargi da hannu a lamarin.

    ''Bayan shafe mako guda, dakarunmu sun kama mutum takwas tare da gano makamai na zamani da kirar gida a ƙauyukan Ratas da Ratoso da kuma Sangasa duka a gundumar Fann da ke yankin ƙaramar hukumar Barikin Ladi'', in ji sanarwar.

    Makaman da aka gano a lokacin samamen sun haɗa da:

    Bindiga ƙirar AK-47, 12 da samufurin AK-47 ƙirar gida 12, da ƙanannan bindigogi 15 da kwanson harsasan AK-47 15 da kakin soja, da harsasai 250 da sauran makamai da kwari da baka da babura bakwai.

  14. Waye zai lashe kyautar Ballon d'Or ta 2024?

    A ranar 4 ga Satumba za a sanar da jerin waɗanda za su yi takarar zama gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na duniya - inda za a yi la'akari da kakar wasa ta 2023-24 tare da kuma manyan gasa da aka gudanar a bazara.

    Yayin da Vinicius Jr da Jude Bellingham na Real Madrid suka kasa lashe gasar cin kofin nahiya da suka buga da Brazil da Ingila, hakan na nufin kambun ya zama na mai rabo ka ɗauka.

    Ga ƴan wasa shida da ake sa ran ɗayan su zai iya yin nasara a bikin da za a yi a ranar 28 ga watan Oktoba a birnin Paris

  15. Yariman Saudiyya ya tattauna da Shugaban Rasha

    Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya tattauna da shugaban Rasha, Vladimir Putin ta wayar hannu.

    Jaridar Saudi Gazzet, ta ruwaito cewa shugabannin biyu sun tattauna yadda za su yauƙaƙa dangantaka tsakankin ƙasashen biyu, tare da yadda za su samar wa ƙasashen ci gaba ta fannoni dban-daban.

    Ƙasashen Rasha da Saudiyya na cikin ƙasashe mafiya arzikin man fetur a duiya.

    Shugaban Rasha dai na ƙoƙarin kunlla ƙawance da ƙasashen yankin Asiya, bayan samun tsamin dangantaka tsakanin ƙasarsa da ƙasashen Yamma kan batun yaƙin Ukraine.

  16. Ana zargin mahaifi da kashe ɗansa bayan lakaɗa masa duka

    Rundunar 'yansanda jihar Legas dake kudancin Najeriya ta ce ta ƙaddamar da bincike kan mutuwar wani matashi mai shekara19, da ake zargin ya mutu sakamakon dukan da mahaifinsa ya yi masa.

    Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Benjamin Hundeyin, ya fitar ya ce rundunar 'yan sanda ta karbi rahoton ƙorafin zargin mahaifin ranar Talata.

    Ya ce mahaifn mai suna Olumide ya ji wa ɗan nasa, Adeyemi rauni sakamakon dukan da ya yi masa da shebur kan wani laifin da ba a bayyana ba.

    Hundeyin ya ce matashin ya ji mummunan rauni a hannunsa sakamakon dukan.

    “An garzaya da matashin zuwa asibiti don ba shi kulawar da ta dace, amma daga can sai aka tura su zuwa babban asibitin Ikeja sakamakon girman ciwon, inda a nan ne ya mutu sakamakon kamuwa da cutar tetanos, kamar yadda likitoci suka bayyana'', in ji sanarwar 'yan sandan.

    'Yansanda sun ce tuni suka kama mahaifin domin gudanar da bincike.

  17. 'Yansandan Kenya sun haramta zang-zanga a Nairobi

    Ƴansandan Kenya sun haramta zanga-zanga a ƙwaryar birnin Nairobi da kewaye har sai abin da hali ya yi la'akari da rashin jagoranci da rundunar 'yansandan ƙasar fuskanta bayan ajiye aiki da shugabanta ya yi, lamarin da rundunar ta ce na kawo mata tarnaƙi a aikinta.

    Haramcin na zuwa ne wata guda bayan zanga-zangar nuna adawa da wasu manufofin gwamnati, wadda ta yi sanadin mutuwar gomman masu zanga-zangar.

    An shirya ƙaddamar da wata zanga-zangar a yau Alhamis a wajen shaƙatawa na Uhuru da ke tsakiyar birnin Nairobi, inda daga nan ne za su yi tattaki zuwa gigan gwamnati da shugaban ƙasar ke zama.

    Nairobi ta kasance cibiyar zanga-zangar da matasan ƙasar ke yi wadda ta bazu zuwa sauran sassan ƙasar.

    Zanga-zangar ta fara ne kan ƙin amincewa da ƙarin haraji da gwamnatin ƙasar ke son yi.

    Bayan gwamnatin ta janye ƙudurin nata ne, kuma matasan suka koma zanga-zangar neman shugaban ƙasar, William Ruto ya sauka daga mulki.

    A yanzu haka an ajiye jami'an tsaro masu yawa a sassan birnin gabanin zanga-zangar.

  18. Ɗaliban Najeriya za su fara karɓar bashin karatu a mako mai zuwa - Nelfund

    Ɗaliban manyan makarantun gwamnatin tarayya a Najeriya da suka nemi bashin kuɗin karatu za su fara samun kuɗin nan da mako ɗaya, a cewar asusun ba da bashin ɗaliban.

    Sai dai shugaban asusun, Akintunde Sawyerr, ya ce ɗaliban makarantun da za su fara sabon zangon karatu ne kawai za su ga kuɗin a asusunsu a yanzu.

    A jiya Laraba ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ƙaddamar da asusun mai suna Nigerian Education Loan Fund (Nelfund) a hukumance a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

    Mista Sawyerr ya ce jimillar ɗalibai 170,000 ne suka yi rajista da asusun, waɗanda suka ƙunshi ɗaliban jami'a, da na kwalejojin ilimi da fasaha.

    "A taƙaice dai, jimillar ɗalibai 110,000 ne suka nemi bashin. Sun ba da bayanansu tare da miƙa takardun neman, kuma su ne suka cancanta. Amma duk da haka za mu ƙara gudanar da bincike a kansu... Amma da alama sama da mutum 110,000 ne za su fara samun bashin a sati mai zuwa," in ji shi.

  19. Asusun IMF zai bai wa Nijar tallafin dala miliyan 71

    Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya sanar ranar Laraba cewa zai bai wa Jamhuriyar Nijar tallafin dala miliyan 255 bayan rikicin tattalin arzikin da ta faɗa sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a shekarar da ta wuce.

    Sanarwar na zuwa ne bayan nazarin da majalisar zartarwar asusun ta yi karo na huɗu da na biyar kan ƙasar ta yammacin Afirka.

    "Matakin zai ba da damar aika dala miliyan 71 lokaci guda," a cewar IMF cikin wata sanarwa, inda jimillar adadin kuɗin da za a bayar za su kai miliyan 255.

    Yayin da ake cigaba da "aiwatar da shirin har zuwa ƙarshen watan Yunin 2023", rikicin siyasar da ƙasar ta faɗa ya jawo tsaiko, abin da ya sa kuɗin ruwa na basukan gida da waje ya taru, in ji asusun.

    "Rikicin siyasa ya yi wa tattalin arzikin Nijar illa matuƙa, da kuma takunkuman da suka biyo bayan juyin mulkin watan Afrilun 2023," kamar yadda asusun ya bayyana.

    IMF na ɗaya daga cikin cibiyoyi ƙalilan na duniya da ba su yanke tallafin da suke bai wa Nijar ba, har ma ta yi hasashen tattalin arzikin ƙasar zai farfaɗo da kashi 10.6 a shekarar nan.

  20. Manyan 'yan jam'iyyar Democrat sun buƙaci Biden ya haƙura da takara

    Kafofin yaɗa labaran Amurka sun bayar da rahoton cewa manyan jagororin jam'iyar Democrat sun buƙaci Shugaba Biden ya janye daga takarar shugaban ƙasa a karo na biyu.

    Suna fargaba cewa jam'iyarsu ka iya rasa rinjaye a dukkan majalisun ƙasar.

    Tsohuwar kakakin majalisar, Nancy Pelosi, da shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Hakeem Jeffries, sun ce sun tattauana da shugaban ƙasar a cikin kwanakin nan.

    Wakilin BBC ya ce rashin nuna karsashi da taɓuka abin kirki a muhawarar ƴantakara ya sanya ana shakku kan cancantar Biden ɗin.

    Bugu da ƙari, yanzu haka dai Shugaba Biden ya kamu da cutar korona.